Aminiya:
2025-07-24@03:31:59 GMT

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda

Published: 4th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Sallah da ke tafe.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, wanda mataimakinsa DCP Saleh Sama’ila ya wakilta, ya bayyana haka ga manema labarai bayan zaman kwamitin tsaron jihar da aka gudanar a Damaturu.

Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike Tinubu ya gana da Fubara a Legas

Taron ya samu jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Baba Malam Wali, a madadin Gwamna Mai Mala Buni.

A cewar CP Emmanuel, rundunar ‘yan sandan tare da sauran hukumomin tsaro sun ɗauki matakan da suka dace don kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sai dai fatan su shi ne Allah Ya sa komai ya tafi lafiya.

Ya ƙara da cewa an tura jami’an tsaro zuwa kowane yanki na jihar tare da umarnin su saka ido sosai da kuma ɗaukar mataki cikin gaggawa idan aka ga wata barazana ga zaman lafiya.

Rundunar ta buƙaci jama’a da su yi bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali ba tare da tayar da wata fitina ba.

Hakazalika, rundunar ta ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda ya nemi tayar da hankali a cikin al’umma.

Taron ya samu halartar babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), da sauran manyan jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bukukuwa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu

Kafafen watsa labarun HKI sun ambato hukumar leken asiri ta “Shabak’ tana sanar da kame wata mace, dake zaune a tsakiyar wannan haramtacciyar kasa bayan da aka tuhumeta da Shirin kashe Fira minister Benjamin Netanyahu.

‘Yan sandan HKI sun ce, matar da aka kama ta so yin amfani da abubuwa masu fashewa da ake kerawa da hannu ( IDE), kuma a halin yanzu  Shabak tana gudanar da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Za Ta Hada Gwiwa FMBN Don Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi
  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho