Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
Published: 4th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Sallah da ke tafe.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, wanda mataimakinsa DCP Saleh Sama’ila ya wakilta, ya bayyana haka ga manema labarai bayan zaman kwamitin tsaron jihar da aka gudanar a Damaturu.
Taron ya samu jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Baba Malam Wali, a madadin Gwamna Mai Mala Buni.
A cewar CP Emmanuel, rundunar ‘yan sandan tare da sauran hukumomin tsaro sun ɗauki matakan da suka dace don kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sai dai fatan su shi ne Allah Ya sa komai ya tafi lafiya.
Ya ƙara da cewa an tura jami’an tsaro zuwa kowane yanki na jihar tare da umarnin su saka ido sosai da kuma ɗaukar mataki cikin gaggawa idan aka ga wata barazana ga zaman lafiya.
Rundunar ta buƙaci jama’a da su yi bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali ba tare da tayar da wata fitina ba.
Hakazalika, rundunar ta ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda ya nemi tayar da hankali a cikin al’umma.
Taron ya samu halartar babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), da sauran manyan jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bukukuwa Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp