Aminiya:
2025-09-17@21:52:08 GMT

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda

Published: 4th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Sallah da ke tafe.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, wanda mataimakinsa DCP Saleh Sama’ila ya wakilta, ya bayyana haka ga manema labarai bayan zaman kwamitin tsaron jihar da aka gudanar a Damaturu.

Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike Tinubu ya gana da Fubara a Legas

Taron ya samu jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Baba Malam Wali, a madadin Gwamna Mai Mala Buni.

A cewar CP Emmanuel, rundunar ‘yan sandan tare da sauran hukumomin tsaro sun ɗauki matakan da suka dace don kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sai dai fatan su shi ne Allah Ya sa komai ya tafi lafiya.

Ya ƙara da cewa an tura jami’an tsaro zuwa kowane yanki na jihar tare da umarnin su saka ido sosai da kuma ɗaukar mataki cikin gaggawa idan aka ga wata barazana ga zaman lafiya.

Rundunar ta buƙaci jama’a da su yi bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali ba tare da tayar da wata fitina ba.

Hakazalika, rundunar ta ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda ya nemi tayar da hankali a cikin al’umma.

Taron ya samu halartar babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), da sauran manyan jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bukukuwa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin