Aminiya:
2025-06-18@01:38:14 GMT

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda

Published: 4th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan Sallah da ke tafe.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, wanda mataimakinsa DCP Saleh Sama’ila ya wakilta, ya bayyana haka ga manema labarai bayan zaman kwamitin tsaron jihar da aka gudanar a Damaturu.

Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike Tinubu ya gana da Fubara a Legas

Taron ya samu jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Baba Malam Wali, a madadin Gwamna Mai Mala Buni.

A cewar CP Emmanuel, rundunar ‘yan sandan tare da sauran hukumomin tsaro sun ɗauki matakan da suka dace don kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sai dai fatan su shi ne Allah Ya sa komai ya tafi lafiya.

Ya ƙara da cewa an tura jami’an tsaro zuwa kowane yanki na jihar tare da umarnin su saka ido sosai da kuma ɗaukar mataki cikin gaggawa idan aka ga wata barazana ga zaman lafiya.

Rundunar ta buƙaci jama’a da su yi bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali ba tare da tayar da wata fitina ba.

Hakazalika, rundunar ta ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda ya nemi tayar da hankali a cikin al’umma.

Taron ya samu halartar babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), da sauran manyan jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bukukuwa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano

Karfafa hulda da al’umma da shugabannin yankuna don samun shawarwari kan inganta tsaro.

Ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki don samun nasara a yaki da daba.

Kwamishinan ‘Yansanda ya tabbatar wa mazauna Kano cewa hukumar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyinsu, inda ya ce za su ci gaba da more zaman lafiya ba tare da fargaba ba. Haka kuma, hukumar ta bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani abin da suka gani na zargi ta layukan gaggawa: 08032419754, 08123821575, ko 09029292926.

Rahotanni sun nuna karuwar ayyukan daba a Kano, musamman a cikin birnin, wanda ke janyo asarar rayuka da raunuka ga ‘yan daba da fararen hula.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa