HausaTv:
2025-06-18@13:31:22 GMT

Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare kan Siriya

Published: 3rd, May 2025 GMT

Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare ta sama kan yankuna daban-daban na kasar Siriya a yammacin Juma’a.

Rahotanni cikin gida sun ruwaito cewa jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare akalla 20 a wajen garuruwan Damascus, Daraa da Hama, inda suka auna wuraren sojoji da ma’ajiyar kaya.  

Hare-haren sun hada da wani sansanin sojojin Syria da ke kusa da kauyen Shatha da ke Hama, hedkwatar tsohuwar bataliyar sojojin Syria da ke arewacin Damascus, da kuma sansanonin soji a Dera.

Fashe-fashe sun afku a Damascus da kewaye, ciki har da Harasta, inda wani farar hula ya mutu.

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ruwaito cewa an kai hari a wasu yankuna a babban birnin kasar a karon farko.

Tun bayan faduwar gwamnatin Bashar al-Assad a watan Disambar 2024, kasar Siriya ta kasance karkashin mamayar Isra’ila.

Da sanyin safiyar Juma’a ne jiragen yakin Isra’ila suka kai hari a yankin da ke kusa da fadar shugaban kasa a Damascus, wanda shi ne hari na biyu da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai a cikin wannan mako.

Hukumomin Isra’ila sun kare harin a matsayin goyon baya ga al’ummar Druze, wadanda ke fafatawa da wasu masu dauke da makamai da HTC ke marawa baya a kusa da Damascus a wani sabon tashin hankali na kabilanci a karkashin mulkin HTC.

Rikicin ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump ya ce yana neman ganin an kawo karshen rikicin nukiliyar ƙasar Iran gaba ɗaya, a yayin da aka shiga kwana na biyar a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila. 

Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami’an ƙasarsa zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a game da lamarin.

Ya bayyana haka ne a yayin da yake hawa jirgi domin barin ƙasar Kanada, inda ya halarci taron ƙasashen G7.

A yayin taron, shugabannin ƙasahen sun bayyana Iran a matsayin barazana, da bai kamata a bari ta mallaki makaman nukiliya ba. A ɗaya bangaren kuma sun bayyana ’yancin Isra’ila na kare kanta.

Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala

Trump wanda ya bar taron tun kafin a kammala ya bayyana cewa abin da ke gabansa na wuce batun tsagaita wuta da Amurka ke nema  tsakanin Iran da Isra’ila.

Ya bayyana cewa ƙasashen biyu da a halin yanzu suke ci gaba da yi wa juna luguden bama-bamai ba su sassauta ba, amma ya sha nanata cewa akwai yiwuwar kawo ƙarshen rikicin da wuri, idan Iran ta amince da tayin da Amurka ta yi mata.

Makon jiya ne jiragen Isra’ila suka ƙaddamar da hare-haren ba-zata a Iran inda suka kashe wasu manyan kwamandoji da masana kimiyyar nukiliya.

Isra’ila ta yi iƙirarin karɓe ikon sararin samaniyar Iran, kuma za ta tsananta kai hare-hare a nan gaba.

Hare-haren sun halaka mutane da dama a sassan kasashen biyu.

Rahotanni a cikin dare sun nuna yadda na’urorin tsaron sararin samaniyar Iran ke kakkaɓo makamai a sassan ƙasar.

Rundunar juyin juya halin Musulunci na Iran ta bayyana cewa za ta sake harba tarin rokoki zuwa Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kai Hare-Hare Kan Cibiyoyin Leken Asirin Isra’ila
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • Jami’an Tsaron Kan Iyakar Iran Sun Harbo Jiragen Masara Matuka 44 Na Sojojin H.K.Isra’ila
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba
  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI