Girke-girkenmu Na Azumi
Published: 1st, March 2025 GMT
Mene ne ruwan kanwa?
Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.
Ya ake ruwan kanwa?
Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ramadan ruwan kanwa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa
Akalla ’yan gudun hijira miliyan daya da dubu 400 da ke Arewa maso gabashin Najeriya ne suke fuskantar barazanar yunwa bayan yanje tallafin da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ke bayarwa.
Wani rahoton majalisar a kan abinci da tsaro wanda gwamnatin Najeriya, Shirin Kula da Abinci na Majalisar (FAO) da sauran masu ruwa da tsaki a baya dai sun yi hasashen ’yan Najeriya miliyan 33.1 za su iya fuskantar matsanancin karancin abinci daga tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025.
Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawulHakan dai na nufin a yanzu yan kasar miliyan 34.7 ne ke nan suke cikin barazanar yunwar.
Ofishin Majalisar mai kula da Agaji (UNOCHA), a rahotonsa na mai taken “Najeriya a 2025 bukatun agajinta da kuma hanyoyin magance su” ya yi bayani daki-daki kan kalubalen da ake fuskanta a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe.
Rahoton ya ce akwai akalla yara miliyan daya da dubu 800 da kef ama da matsanancin karancin abinci.
Rahoton ya alakanta hakan da ci gaba da karuwar farashin kayayyaki a Najeriya wanda ya kai kaso 40.9 cikin 100 a watan Yunin 2024.
Kazalika, karuwar adadin na da nasaba da rage tallafin da MDD ke bayarwa ba, sanadiyyar yanke mata kudaden tallafin da musamman Amurka ke bayarwa.