Aminiya:
2025-11-02@00:52:58 GMT

NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC

Published: 20th, February 2025 GMT

Jam’iyyar adawa ta NNPP ta rasa ɗaya daga cikin mambobinta a Majalisar Wakilai zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Gwaram ta Jihar Jigawa, Yusuf Shitu Galambi. Shi ne ɗan jam’iyyar NNPP na farko da ya sauya sheƙa ya koma APC.

Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Idan dai za a iya tunawa, ’yan jam’iyyar adawa na PDP da LP da dama sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

Ɗan Majalisa Galambi ya bayyana cewa, ya bar jam’iyyar NNPP ne saboda rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar wanda ya haifar da wasu ƙararraki da suka shafi ayyukan jam’iyyar.

Ya kuma ƙara da cewa, Jam’iyyar NNPP ta rabu gida biyu sakamakon rigimar mulki tsakanin iyayen jam’iyyar da suka kafa ta, Sanata Rabi’u Musa Kwakwanso da ɗan takararta na Shugaban ƙasa a shekarar 2023, Peter Obi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwaram Jigawa Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35

Majalisar Tarayya, ta amince da buƙatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na karɓo rancen dala biliyan 2.35 domin cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Dukkanin Mjalisun sun amince da buƙatar ne a ranar Laraba, bayan sun duba rahoton kwamitin karɓar basussuka na cikin gida da na waje.

Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya

Haka kuma, majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na fitar da dala miliyan 500 domin samar da muhimman ayyuka kamar faɗaɗa hanyoyin samun kuɗi ga ƙasar nan.

A cikin wasiƙar da ya aike wa majalisar tun a farkon watan nan, Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa neman rancen ya zama dole domin aiwatar da kasafin kuɗin 2025.

Kasafin wanda ya ƙunshi Naira tiriliyan 9.28 na nufin cike giɓin da ake da shi a kasafin 2025.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kauce wa kasa biyan bashi da kuma bin inganta ƙa’idojin kasuwar hada-hadar bashi ta duniya.

“Jimillar kuɗin da za a nema daga waje; dala biliyan 1.229 na sabon rance da dala biliyan 1.118 na sake biyan tsohon bashi zai kai dala biliyan 2.347,” in ji wasiƙar.

’Yan majalisa sun bayyana cewa rancen zai taimaka wa gwamnati ci gaba da aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa da kuma daidaita tattalin arziƙi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
  • Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29
  • Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe
  • Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35