Fim din da aka yi shi da kagaggun hotuna mai suna “Ne Zha 2” ya zama fim din kasar Sin na farko da ya samu zunzurutun kudi har yuan biliyan 10, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.39 bisa jimillar kudadensa da aka samu a duniya, ciki har da na ba da sautonsa, inda ya zarce misalin da aka yi hasashe a ranar Alhamis, bisa bayanan da aka samu daga dandalin sayar da tikiti na Maoyan.

Wannan gagarumar nasarar da aka samu a rana ta 16 bayan fitowar fim din a ranar bikin sabuwar shekara ta kalandar gargajiya ta kasar Sin da ta kasance ranar 29 ga watan Janairu, ta shiga jerin ci gaban da fim din ke samu na kafa tarihi.

“Ne Zha 2” ya riga ya zama fim na farko da ya samu dalar Amurka biliyan 1 a kasuwa guda, sannan ya zama fim din da ba na masana’antar shirya fina-finan Amurka ba da ya shiga sahun masu kambun samar da kudin da ya kai dala biliyan.

Wasu manazarta da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Alhamis, sun bayyana cewa, sun yi imanin nasarar da “Ne Zha 2” ya samu ta zarce batun adadi mai kayatarwa da sashen fina-finan ya bayyana, inda take nuna matukar kuzari, da ban sha’awa, da kuma bajintar al’adun Sinawa da fikirarsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu

A cewarsa, tuni aka shirya wuraren kwana da abinci ga maniyyatan a kasar Saudiyya.

 

Abdulkadir ya tabbatar da cewa, ana shirye-shirye, inda za a yi alluran rigakafi a ranar 28 ga Afrilu, za a raba tufafi a 30 ga Afrilu, sannan kuma za a raba jakunkuna a ranar 1 ga Mayu.

 

Ya kara da cewa maniyyatan da suka biya sama da Naira miliyan 8.4 na kudin aikin Hajji, za a biya su bayan sun dawo daga Saudiyya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu