Fim din da aka yi shi da kagaggun hotuna mai suna “Ne Zha 2” ya zama fim din kasar Sin na farko da ya samu zunzurutun kudi har yuan biliyan 10, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.39 bisa jimillar kudadensa da aka samu a duniya, ciki har da na ba da sautonsa, inda ya zarce misalin da aka yi hasashe a ranar Alhamis, bisa bayanan da aka samu daga dandalin sayar da tikiti na Maoyan.

Wannan gagarumar nasarar da aka samu a rana ta 16 bayan fitowar fim din a ranar bikin sabuwar shekara ta kalandar gargajiya ta kasar Sin da ta kasance ranar 29 ga watan Janairu, ta shiga jerin ci gaban da fim din ke samu na kafa tarihi.

“Ne Zha 2” ya riga ya zama fim na farko da ya samu dalar Amurka biliyan 1 a kasuwa guda, sannan ya zama fim din da ba na masana’antar shirya fina-finan Amurka ba da ya shiga sahun masu kambun samar da kudin da ya kai dala biliyan.

Wasu manazarta da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Alhamis, sun bayyana cewa, sun yi imanin nasarar da “Ne Zha 2” ya samu ta zarce batun adadi mai kayatarwa da sashen fina-finan ya bayyana, inda take nuna matukar kuzari, da ban sha’awa, da kuma bajintar al’adun Sinawa da fikirarsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Kakakin Gwamnatin Iran Ta Ce daga Yau Lahadi Wuraren Fakewa A Bude Suke Sa’o’I 24 A Tehran
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai