Fim din da aka yi shi da kagaggun hotuna mai suna “Ne Zha 2” ya zama fim din kasar Sin na farko da ya samu zunzurutun kudi har yuan biliyan 10, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.39 bisa jimillar kudadensa da aka samu a duniya, ciki har da na ba da sautonsa, inda ya zarce misalin da aka yi hasashe a ranar Alhamis, bisa bayanan da aka samu daga dandalin sayar da tikiti na Maoyan.

Wannan gagarumar nasarar da aka samu a rana ta 16 bayan fitowar fim din a ranar bikin sabuwar shekara ta kalandar gargajiya ta kasar Sin da ta kasance ranar 29 ga watan Janairu, ta shiga jerin ci gaban da fim din ke samu na kafa tarihi.

“Ne Zha 2” ya riga ya zama fim na farko da ya samu dalar Amurka biliyan 1 a kasuwa guda, sannan ya zama fim din da ba na masana’antar shirya fina-finan Amurka ba da ya shiga sahun masu kambun samar da kudin da ya kai dala biliyan.

Wasu manazarta da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Alhamis, sun bayyana cewa, sun yi imanin nasarar da “Ne Zha 2” ya samu ta zarce batun adadi mai kayatarwa da sashen fina-finan ya bayyana, inda take nuna matukar kuzari, da ban sha’awa, da kuma bajintar al’adun Sinawa da fikirarsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato

Wani magidanci, Malam Jibrin Rabi’u, ya bayyana yadda matarsa, Khadijat Ado, ta ɓace a gidansu da ke unguwar Life Camp a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata, sannan kuma aka gano ta a Sakkwato washegari.

Ya shaida wa wakilinmu da yammacin Lahadi, cewa ya dawo gida a ranar Alhamis, sai ya tarar da matarsa ba ta nan.

Malam Jibril ya ce, ya kira wani abokinsa ɗan sanda, wanda ya sanar da ofishin ’yan sanda na Life Camp, Gwarinpa da sauran sassan yankin bayan bincike na farko ya gagara gano inda take.

A cewarsa, na’urar CCTV da ke gidansu ta nuna yadda matarsa ta fita daga gidan cikin natsuwa, har sai da ta fita daga inda kyamarar ke iya ɗauka.

Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe

Malam Jibrin ya ce duk da ƙoƙarin da suka yi na gano ta a ranar Alhamis ɗin, ba su samu nasara ba.

Sai dai ya ce da yammacin Juma’a aka kira shi aka shaida masa cewa an gano matarsa a Sakkwato, amma ba ta iya magana.

Ya ce, “Yanzu ma har yanzu ba ta iya magana ba, amma ta dawo cikin hayyacinta. Muna tattaunawa ta hanyar rubutu ne kawai.”

Ya bayyana cewa matarsa ta rubuto masa cewa a ranar da ta ɓace, ta ji kamar wani ana kiranta ne, sai ta buɗe ƙofa ta fita — daga nan kuma ba ta san abin da ya faru ba, sai da ta tsinci kanta a Sakkwato.

A cewar Malam Jibrin, “Ta ce da ta isa Sakkwato, ta haɗu da wata mace wadda ta roƙi takarda da biro, sannan ta rubuta mata abin da ya faru domin ba ta iya magana.”

Ya ce daga nan ne wannan matar ta kira shi, inda ya nemi ta da ta kai matarsa wurin danginsa da ke Sakkwato.

Malam Jibrin ya ce har yanzu matarsa tana Sakkwato, kuma ba ta samu damar yin magana ba, amma ya shirya tafiya Sakkwato yau domin ya dawo da ita gida.

Wata majiyar ’yan sanda a Life Camp ya tabbatar da cewa an kawo rahoton ɓacewar a ranar Alhamis, amma ya ce duk wani ƙarin bayani sai an tuntuɓi hedikwatar rundunar.

An kuma bayyana cewa kiraye-kirayen da aka yi wa jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Abuja, DSP Josephine Adeh, ba ta ɗaga wayarta ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump
  • Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar