Aminiya:
2025-08-01@16:06:08 GMT

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya

Published: 6th, February 2025 GMT

Kwamitin Sake Duba Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na Majalisar Wakilai, ya bayar da shawarar ƙirƙiro sabbin jihohi 31 domin ƙara yawan jihohin ƙasar nan daga 36 zuwa 67.

Shugaban kwamitin, wanda kuma shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Benjamin Okezie Kalu ne, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya jagoranta a ranar Alhamis.

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi  Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

Daga cikin sabbin jihohin da aka bayar da shawarar ƙirƙirar su, akwai Benue Ala, Okun, Okura, Confluence, Apa-Agba, Apa da Abuja, waɗanda za a samar daga jihohin Benuwe da Kogi, tare da babban Birnin Tarayya.

A Arewa Maso Gabas, an bayar da shawarar ƙirƙiro jihohin Amana daga Jihar Adamawa, Katagum daga Bauchi, Savannah daga Borno, da Muri daga Taraba.

A Arewa Maso Yamma, akwai jihohin New Kaduna da Gurara daga Kaduna, Tiga da Ghari daga Kano, da kuma Kainji daga Kebbi.

A Kudu Maso Gabas kuwa, akwai jihohin Etiti, Urashi, Orlu, Aba da Adada, waɗanda za su fito daga yankin gaba ɗaya.

A yankin Kudu Maso Kudu, ana son ƙirƙiro jihohin Ogoja daga Kuros Riba, Warri daga Delta, Bori daga Ribas, da Obolo daga Ribas da Akwa Ibom.

A Kudu Maso Yamma, an tsara sabbin jihohin Toru-Ebe daga Delta, Edo da Ondo, Ibadan daga Oyo, Lagoon daga Legas, Ijebu daga Ogun, Oke-Ogun daga Ogun, Oyo da Osun, da Ife-Ijesha daga Ogun, Oyo da Osun.

Idan wannan shawara ta samu amincewa, Najeriya za ta ƙara yawan jihohinta daga 36 zuwa 67.

Ana kyautata zaton lamarin zai kawo sauyi mafi girma a tsarin gudanarwar Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Ghari Majalisar Wakilan Najeriya Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin watanni shidan farko na bana, an kafa sabbin kamfanoni 30,014 na masu zuba jari daga kasashen waje a babban yankin kasar Sin, wanda ya nuna karuwar hakan da kashi 11.7 cikin dari a mizanin duk shekara.

Kazalika, bayanai sun nuna cewa, saka hannun jari daga kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya ya karu da kaso 8.8 cikin dari a tsakanin lokacin.

Har ila yau, jarin da aka zuba daga kasar Switzerland ya karu da kaso 68.6, na Japan ya karu da kashi 59.1, na Birtaniya ya karu da kaso 37.6, sai kuma na Jamus da ya karu da kashi 6.3, kana wanda aka zuba daga Jamhuriyar Koriya kuma ya karu da kashi 2.7 bisa dari. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana