Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Karfafa Asun Horar Da Ma’aikata
Published: 4th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za ta karfafa kyakkyawar alakar da ke tsakaninta da asusun horar da ma’aikata ITF.
Shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Muhammad K Dagaceri ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban asusun horas da ma’aikata na yankin arewa maso yamma, Malam Aminu Abdu a ofishinsa.
A cewarsa, gwamnatin jihar tana sane da muhimmancin da asusun ke da shi, musamman ga ma’aikatan da aka horas da su domin samun kwarewa a fanninsu.
Dagaceri, ya tabbatar wa shugaban asusun cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da bayar da dukkan goyon baya da hadin kai ga sabon ofishin na ITF da aka kafa a yankin Jigawa.
Tun da farko, Shugaban Asusun na Arewa maso Yamma, Malam Aminu Abdu ya ce sun kawo ziyarar ne a madadin babban daraktan asusun, domin nuna jin dadinsu ga Gwamna Umar Namadi bisa yadda ya samar wa sabon ofishinsu da aka kafa a yankin na Jigawa.
Aminu Abdu ya kara da cewa, asusun ya horar da ma’aikata a fadin kasar nan, kuma kwalliya na biyan kudin sabulu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
A yau Laraba sa jijjifin Safiya an sami shahidai 3 a Gaza da hakan ya kara yawan shahidai zuwa 40 a cikin sa’o’i 24.
Bugu da kari, baya ga shahidan da suke faduwa a kowace rana, ana fama da matsananciyar yunwa a cikin yankin, bayan karewar kayan abincin HKI ta sake komawa yaki kwanaki 44 da su ka gabata.
A cikin sansanin ‘yan hijira na “Nusairat” mutane 3 sun yi shahada da su ka hada da karamar yarinya sanadiyyar harin da sojojin na HKI su ka kai wa yankin.
A gabashin birnin Khan-Yunus ma dai wasu Falasdinawa sun yi shahada.
Daga ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu adadin wadanda su ka yi shahada sun wuce 52,000,wadanda su ka jikkata kuma sun haura 100,000.