More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan da Gwamnatin Kano ta sanar cewa ta ware Naira biliyan biyu da rabi don aura da ’yan mata da zawarawa a jihar batun ke ta shan suka daga ɓangarori daba-daban.

Wasu na ganin jihar na da wasu buƙatun da suka fi auren gatan muhimmanci da ya kamata gwamnatin ta fi mayar da hankali a kansu.

NAJERIYA A YAU: Anya Jam’iyyar PDP Za Ta Kai Labari A Fagen Siyasar Najeriya Kuwa? DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana ya yi nazari ne kan dalilan da Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan biyu da rabi don aurar da ’yan mata da zawarawa.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan mata Hukumar Hisbah

এছাড়াও পড়ুন:

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

 

Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.

 

Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.

 

Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.

 

Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.

 

Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?

 

Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.

 

Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani October 28, 2025 Ra'ayi Riga Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka? October 27, 2025 Ra'ayi Riga Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata October 23, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba