Van Rompuy: Ya Kamata A Kiyaye Cudanya Tsakanin Mabambantan Al’adu
Published: 1st, February 2025 GMT
Wakilin CMG ya yi hira da tsohon shugaban majalisar nahiyar Turai, kuma tsohon firaministan kasar Belgium, Herman Van Rompuy, a kwanan baya, inda tsohon shugaban ya nanata bukatar karfafa cudanya tsakanin al’adun bangarorin yammaci da gabashin duniya.
Herman Rompuy ya ce, ta hanyar cudanya, kowa zai iya koyon sabbin dabarun da yake bukata, kana za a iya tabbatar da fahimtar juna.
Dangane da shawarar raya “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar, Mista Rompuy ya ce, ana bukatar tabbatar da saukin jigilar kayayyaki tsakanin kasashe daban daban, gami da ingancin cinikin duniya, ganin yadda suka jibanci wadatar al’ummun kasashen duniya. Saboda haka, yana goyon bayan duk wani matakin da zai amfanawa karfafar hadewar sassan duniya.
Ban da haka, tsohon dan siyasan na nahiyar Turai ya yi tsokaci kan shawarwarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, dangane da yunkurin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da ingancin cudanyar al’adu a duniya, inda ya ce, shawarwari sun nuna burikan da ake neman cimmawa a kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa baki daya. Ya ce, dukkan kasar Sin da kasashen Turai za su iya samar da gudunmowa ga yunkurin cimma wadannan manyan burika masu muhimmanci. (Bello Wang)
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta bayyana cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila’ tana aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa ana gani kai tsaye a tauraron dan Adam
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International a yau Talata ta yi Allah wadai da shirun da duniya ta yi game da yadda gwamnatin yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya take aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, kai tsaye duniya na gani ta hanyar tauraron dan Adama.
A yayin gabatar da rahoton shekara-shekara na kungiyar ta Amnesty kan kare hakkin bil’adama a duniya Agnes Callamard, sakatariyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International, ta ce tun ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, duniya ke kallon yadda ake aiwatar da kisan kare dangi kai tsaye a tauraron dan Adam a Zirin Gaza.
Ta kara da cewa, “Sun ga kasashe kamar babu abin da zasu iya saboda da rauni” tare da nuna cewa “gwamnatin mamayar Isra’ila na kashe dubban Falasdinawa maza da mata, ta hanyar kisan kiyashi kan dukkanin iyalai da suka hada da kananan yara, da lalata gidaje, rusa cibiyoyin tsare rayuka, rusa asibitoci da cibiyoyin ilimi.