Leadership News Hausa:
2025-06-16@10:52:49 GMT

Van Rompuy: Ya Kamata A Kiyaye Cudanya Tsakanin Mabambantan Al’adu

Published: 1st, February 2025 GMT

Van Rompuy: Ya Kamata A Kiyaye Cudanya Tsakanin Mabambantan Al’adu

Wakilin CMG ya yi hira da tsohon shugaban majalisar nahiyar Turai, kuma tsohon firaministan kasar Belgium, Herman Van Rompuy, a kwanan baya, inda tsohon shugaban ya nanata bukatar karfafa cudanya tsakanin al’adun bangarorin yammaci da gabashin duniya.

Herman Rompuy ya ce, ta hanyar cudanya, kowa zai iya koyon sabbin dabarun da yake bukata, kana za a iya tabbatar da fahimtar juna.

A daura da haka, idan an yi watsi da damar cudanya da tattaunawa, to, tabbas za a samu abkuwar rikici da arangama, har ma zai kai ga barkewar yake-yake.

Aston Villa Na Neman Ɗaukar Marcus Rashford A Matsayin Aro  AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

Dangane da shawarar raya “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar, Mista Rompuy ya ce, ana bukatar tabbatar da saukin jigilar kayayyaki tsakanin kasashe daban daban, gami da ingancin cinikin duniya, ganin yadda suka jibanci wadatar al’ummun kasashen duniya. Saboda haka, yana goyon bayan duk wani matakin da zai amfanawa karfafar hadewar sassan duniya.

Ban da haka, tsohon dan siyasan na nahiyar Turai ya yi tsokaci kan shawarwarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, dangane da yunkurin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da ingancin cudanyar al’adu a duniya, inda ya ce, shawarwari sun nuna burikan da ake neman cimmawa a kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa baki daya. Ya ce, dukkan kasar Sin da kasashen Turai za su iya samar da gudunmowa ga yunkurin cimma wadannan manyan burika masu muhimmanci. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin