Amurka Zata Fitar Da Dokar Hukunta Kotun Kasa Da Kasa Saboda Zargin Isra’ila Da Kotun Ya Yi
Published: 29th, January 2025 GMT
Majalisar Dokokin Amurka zata dauki matakin fitar da dokar da zata hukunta kotun hukunta manyan laifuka ta duniya saboda kotun ta tabbatar da zarge-zargen manyan laifukan gwamnatin mamayar Isra’ila
Ana sa ran nan kusa kadan Majalisar Dattawan Amurka za ta fara kada kuri’a kan kakaba takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta duniya da ke birnin Hague, bayan da kotun ta tuhumi fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohun ministan yakinsa Yoav Gallant a watan Mayu da aikata laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Zirin Gaza.
A cewar jaridar Washington Post, ‘yan majalisar dokokin Amurka suna matsawa wajen zartar da dokar, wadda za ta sanya takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa, yayin da wasu daga cikin manyan kawayen Amurka na kasashen Turai suke fargabar cewa: Dokar za ta gurgunta babbar kotun hukunta manyan laifukan ta duniya tare da baiwa masu aikata laifukan yaki damar cin karensu ba babbaka ba tare hukunta su ba, kuma hakan zai raunana mutuncin kasashen yamma”.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kotun hukunta manyan
এছাড়াও পড়ুন:
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp