Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA
Published: 16th, March 2025 GMT
Shugaba Donald Trump na Amurka ya ba da umarnin dakatar da ayyukan wasu hukumomin ƙasar guda shida da rushe wasu baki ɗaya, ciki har da kafar yaɗa labarai ta Voice of America wato VOA.
Sauran hukumomin sun haɗa da gidajen adana kayan tarihi da ɗakunan karatu da ɓangaren kula da marasa galihu da ke kwana kan tituna.
Daraktan Muryar Amurka, Mike Abramowitz, ya ce an aike kusan dukkanin ma’aikatan hutun dole na sai baba ta gani.
Sannan kuɗaɗen da ake warewa wajen tafiyar da kafofin da ke ƙarƙashinta, irinsu Gidan Rediyon Turai da Asia da kuma Liberty an dakatar da su baki ɗaya.
Babu dai wani takamaiman bayani daga gwamnatin Amurka kan me hakan ke nufi, sannan babu wanda zai iya fahimtar ko an rufe kafofin baki ɗaya ke nan.
Shugaban ƙungiyar ’yan jarida a Amurka, William McCarren ya ce wannan ba abin alheri ba ne ga duniya da kuma aikin jarida baki ɗaya, musamman a wannan zamani da ake yaƙi da labaran bogi.
Tuni dai Shugaba Trump ya naɗa ’yar jarida Kari Lake a matsayin daraktar hukumar da za ta kula da rushe waɗannan hukumomi, waɗanda ya zarga da yaɗa labaran nuna masa ƙiyayya.
Sama da shekaru 80 ke nan da kafa VOA wadda ke yaɗa shirye-shiyenta cikin harsuna 40, ta rediyo da talabijin da intanet da shafukan zumunta na zamani.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), ta kammala fitar da jadawalin Rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026.
Za a gudanar da gasar ne a Amurka, Kanada da Mexico daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026.
Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan KwaraRabon jadawalin ya gudana ne a birnin Washington na ƙasar Amurka a ranar Juma’a, inda Ingila ta samu kanta a rukuni ɗaya Croatia.
Brazil za ta kara da Maroko, yayin da Amurka za ta kara da Australia.
Faransa za ta ɓarje gumi da Senegal, sannan Argentina za ta fafata da Austria.
Ga jerin yadda kowane rukuni na gasar Kofin Duniya na 2026 ya kasance:
Rukuni A: Mexico, Afirka ta Kudu, Koriya ta Kudu, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.
Rukuni B: Kanada, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Qatar, Switzerland
Rukuni C: Brazil, Maroko, Haiti, Scotland
Rukuni D: Amurka, Paraguay, Australia, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar.
Rukuni E: Jamus, Curaçao, Ivory Coast, Ecuador.
Rukuni F: Netherlands, Japan, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Tunisia.
Rukuni G: Belgium, Masar, Iran, New Zealand.
Rukuni H: Spain, Cape Verde, Saudi Arabia, Uruguay
Rukuni I: Faransa, Senegal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Norway
Rukuni J: Argentina, Aljeriya, Austria, Jordan.
Rukuni K: Portugal, ƙasar da ta samu gurbin zuwa gasar, Uzbekistan, Colombia
Rukuni L: Ingila, Croatia, Ghana, Panama