Aminiya:
2025-04-30@23:24:52 GMT

Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

Published: 16th, March 2025 GMT

Shugaba Donald Trump na Amurka ya ba da umarnin dakatar da ayyukan wasu hukumomin ƙasar guda shida da rushe wasu baki ɗaya, ciki har da kafar yaɗa labarai ta Voice of America wato VOA.

Sauran hukumomin sun haɗa da gidajen adana kayan tarihi da ɗakunan karatu da ɓangaren kula da marasa galihu da ke kwana kan tituna.

Mahaifiyar Sarkin Gwoza ta rasu Yadda za a girka ‘Kamoniya’

Daraktan Muryar Amurka, Mike Abramowitz, ya ce an aike kusan dukkanin ma’aikatan hutun dole na sai baba ta gani.

Sannan kuɗaɗen da ake warewa wajen tafiyar da kafofin da ke ƙarƙashinta, irinsu Gidan Rediyon Turai da Asia da kuma Liberty an dakatar da su baki ɗaya.

Babu dai wani takamaiman bayani daga gwamnatin Amurka kan me hakan ke nufi, sannan babu wanda zai iya fahimtar ko an rufe kafofin baki ɗaya ke nan.

Shugaban ƙungiyar ’yan jarida a Amurka, William McCarren ya ce wannan ba abin alheri ba ne ga duniya da kuma aikin jarida baki ɗaya, musamman a wannan zamani da ake yaƙi da labaran bogi.

Tuni dai Shugaba Trump ya naɗa ’yar jarida Kari Lake a matsayin daraktar hukumar da za ta kula da rushe waɗannan hukumomi, waɗanda ya zarga da yaɗa labaran nuna masa ƙiyayya.

Sama da shekaru 80 ke nan da kafa VOA wadda ke yaɗa shirye-shiyenta cikin harsuna 40, ta rediyo da talabijin da intanet da shafukan zumunta na zamani.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.

A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.

Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.

Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.

Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114