Ma’aikatar Tsaron Jama’ar Sin Na Matukar Adawa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Karin Haraji
Published: 1st, March 2025 GMT
A jiya Juma’a ne mai magana da yawun ma’aikatar tsaron jama’a ta kasar Sin ya bayyana rashin amincewa da barazanar da Amurka ta yi ta sanya karin harajin kashi 10 cikin dari kan kayayyakin da kasar Sin ke fitarwa. Ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga wata tambayar manema labarai kan barazanar karin haraji da Amurka ta yi, wanda zai fara aiki daga ranar 4 ga Maris, kuma ta ambaci matsalar fentanyl a matsayin dalilin.
Kakakin ya ce, kasar Sin ta ba da goyon baya ga Amurka wajen tinkarar matsalar fentanyl bisa dalilan jin kai, kuma ta samu sakamako mai kyau. Ya kara da cewa, rikicin fentanyl matsala ce da tushenta ke cikin Amurka. Yana mai cewa, bangaren Amurka ya yi watsi da hakikanin gaskiya kuma ya kasa magance ainihin batutuwan da suka shafi bukatun miyagun kwayoyi yayin da yake dora laifin kan wasu kasashe. Abin da Amurka take yi ba zai taimaka wajen magance matsalar ba, kuma zai yi illa sosai ga hadin gwiwar Sin da Amurka kan yaki da muggan kwayoyi. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan kalaman da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi game da Najeriya.
Kwankwaso, ya yi wannan magana ne bayan Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi game da zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.
Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da AmurkaA cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya ce Najeriya ƙasa ce mai cikakken ’yanci, wadda ke fama da matsalar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar.
“Matsalar tsaron da muke fuskanta ba ta bambanta tsakanin addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji shi.
Ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta tallafa wa Najeriya da sabbin fasahohi domin yaƙar matsalar tsaro maimakon yin kalaman da za su iya raba kan ’yan ƙasa.
“Amurka ya kamata ta taimaka wa hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance matsalolin tsaro, maimakon yin barazanar da za ta ƙara raba ƙasar,” in ji Kwankwaso.
Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Najeriya da ta naɗa jakadu na musamman domin inganta hulɗar diflomasiyya da Amurka da kare muradun ƙasar a matakin duniya.
Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su zauna lafiya, inda ya bayyana cewa wannan lokaci ne da ya dace a fifita haɗin kan ƙasa ba abin da ke raba ta ba.
“Wannan lokaci ne da ya kamata mu mayar da hankali kan abin da zai haɗa kanmu ba wanda zai raba mu ba. Allah Ya albarkaci Najeriya,” in ji shi.