Aminiya:
2025-06-15@23:18:23 GMT

Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa

Published: 27th, February 2025 GMT

Wasu gungun ‘yan Boko Haram ɗauke da muggan makamai sun kai farmaki cikin dare a garin Kwapre da ƙauyukan da ke gundumar New Yadul a ƙaramar hukumar Hong a Jihar Adamawa.

Harin wanda ya fara daga misalin ƙarfe 7:30 na yammacin ranar Talata, 25 ga watan Fabrairu, kuma ya ɓarnata dukiyoyi a tsakiyar daren.

Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno

Al’ummar yankin sun ce, an ƙona wuraren ibada da makarantu da gidaje da wuraren kasuwanci, sannan an wawushe dukiyoyi na miliyoyin Naira.

Mista Joel Kulaha, Hakimin garin Kwapre da Abalis Jawaja, kuma dagacin ƙauyen, ya ce maharan sun farwa al’ummar garin, inda suka ƙona gine-gine tare da kwashe kayayyaki masu daraja.

Sun ce, an yi sa’a ba a rasa rayuka a harin ba, domin mazauna yankin sun yi gargaɗin ƙaruwar barazanar harin, sun tsere daga gidajensu kafin maharan su iso.

“Mun tsere da rayukanmu, amma duk abin da muka mallaka ya tafi,” kamar yadda Kulaha ya koka, yana kwatanta harin da aka kai.

An samu rahoton cewa dakarun sojin da ke kusa da Garaha sun mayar da martani kan harin da sanyin safiya, inda suka fatattaki maharan.

Sai dai mazauna yankin sun ce matakin sojan ya makara ne domin daƙile ɓarnar da ta ɓarke ƙauyukan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Kwapre Hong

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka

An samu cece-ku-ce a Jihar Sakkwato bayan da wata jita-jita ta yaɗu cewa Mataimakin Gwamnan jihar, ya karɓi shanu 400 da aka tanadar domin tallafa wa marasa galihu domin yin layya a lokacin Sallah Babba.

An ce shanun wata ƙungiya ce daga ƙasar Turkiyya ta bayar da su, ta hannun Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, domin tallafa wa waɗanda ba su da halin yin layya.

Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna

Sai dai an zargi Mataimakin Gwamnan da karɓe su don amfanin kansa.

Wannan batu ya jawo jama’a a jihar suk dinga bayyana ra’ayoyinsu, inda wasu ke zargin an fifita jami’an gwamnati fiye da talakawa da aka yi nufin bai qa shanun.

Wasu sun zargi cewa malamai, limamai, ‘yan siyasa da ƙungiyoyin addini ne suka fi cin moriyar shanun.

Sai dai a wata hira da wakilinmu ya yi, da mataimakin gwamnan ya musanta karɓar shanun.

Ya ce: “Hukumar Zakka ce ke raba wa ’yan gudun hijira da ke fama da matsalar tsaro kamar a Sabon Birni da Isa.

“A shekarar da ta gabata sun karɓi shanu 20 kowane. Haka nan Illela da Gwadabawa sun samu goma-goma.”

Ya ƙara da cewa ba shi da hannu kai-tsaye, domin an tuntuɓar shi ne kawai a matsayin wanda zai jagoranci rarraba shanun ga jama’ar yankin da ke ƙarƙashinsa.

Shugaban Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, Malam Muhammad Lawal Maidoki, ya ƙara bayyana cewa:

“Mataimakin gwamna bai karɓi shanun ba. An kafa kwamiti ƙarƙashinsa domin kula da rabon a yankin Gabas da ke fama da matsalar tsaro. Shanun sun ƙare kafin a gama rabawa. An ware 150, amma 106 ne aka samu.”

Ya kuma bayyana cewa sun yi niyyar yanka shanu 4,500 amma saboda wasu matsaloli, ciki har da rashin samun dabbobi da suka cika sharuɗan layya, sun yanka 3,000 kacal.

Malam Maidoki ya nemi afuwa ga duk wanda bai samu shanun ba, da waɗanda aka saba bai wa amma aka kasa ba su, da waɗanda suke tsammanin samun amma ba su samu ba.

Ya ƙara da cewa sun rubuta sunayen waɗanda ba su samu ba domin tunawa da su a shekara mai zuwa.

“Muna fata Allah Ya kawo mu wata shekara cikin lafiya da dama don ci gaba da tallafa wa marasa ƙarfi a irin wannan lokaci,” in ji shi.

A cewar hukumar, shirin ya laƙume sama da Naira biliyan ɗaya, kuma an raba naman layya ga dubban mutane da ba su samu damar yin yanka ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar