Jirgin Saman Da Kasar Sin Ta Kera Mai Amfani Da Lantarki Ya Yi Tashin Farko Cikin Nasara
Published: 21st, February 2025 GMT
A yau Jumma’a ne jirgin saman da kasar Sin ta kera samfurin AS700D mai amfani da makamashin lantarki ya kammala tashinsa na farko cikin nasara, wanda ya nuna sabon ci gaban da kasar ta samu a sashen samar da kayayyakin sufurin jiragen sama masu amfani da makamashi mai tsafta a fannin tattalin arzikin jirage masu tashi kasa-kasa daga doron kasa, kamar yadda kamfanin sarrafa jiragen sama na kasar Sin (AVIC) wanda ya kera jirgin ya sanar.
Kamfanin AVIC ya bayyana cewa, wannan muhimmin ci gaba ya tabbatar da girman iya kere-kere da ka’idoji na kasar Sin bisa kera jirgin na AS700D da kanta ba tare da sa hannun kowa ba, tare da samar da tanadin da ake bukata na fasaha don bunkasa kera jirage masu amfani da makamashin lantarki da za su biyo baya.
Jirgin na AS700D ya gudanar da tashin na farko ne da safiyar yau Juma’a a Jingmen na lardin Hubei da ke tsakiyar kasar Sin.
Bayanai sun nuna jirgin ya tashi sannu a hankali a tsaye sannan ya yi sauri ya nausa zuwa tsayin mita 50. Bayan ya yi shawagi a takaice, sai ya sauka a tsaye kana daga bisani ya tsaya sannu a hankali. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.
Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.
Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”
Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.
Tun da fari, Fira ministan kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa; A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta yi matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.
Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.