Shugaban kasar Iran da Sarkin kasar Qatar sun jaddada muhimmancin hadin gwiwa da taimakekkeniya tsakanin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamid Al Thani sun gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Tehran, inda suka jaddada karfin dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma muhimmancin kara inganta taimakekkeniya a tsakanin kasashensu.

Shugaban na Iran ya fada a yammacin yau Laraba cewa: Ci gaba da tarukan tsakanin jami’an kasashen biyu ke yi na tabbatar da kyakkyawar alakar da ke tsakaninsu, yana mai jaddada karfafa alaka da kasashe makwabta, musamman kasar Qatar, a matsayin wani muhimmin ka’ida na manufofin ketare na Iran.

Shugaban kasar ya ci gaba da cewa: Sun tattauna da Sarkin Qatar kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu ta hanyar da za ta tabbatar da moriyar kasashensu, kuma an yanke wasu muhimman shawarwari na raya kasa da zurfafa dangantaka da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Sarkin Qatar ya kuma jaddada bukatar samar da sabbin damar gudanar da hadin gwiwa.

Shugaba Pezeshkian ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi imanin cewa, kasashen yankin suna da karfin daukar matakai na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, bisa tushen kyakkyawar makwabtaka da mutunta juna da kyautata mu’amala mai ma’ana, da share fagen kafa wani tsari na hadin gwiwa da taimakekkeniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Shugaban kasar hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu

Shugaban kasar Ivory Coast Alhassan Outtara ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a karo na 4 wanda za a gudanar a watan Oktoba mai zuwa.

Za a yi manyan zabukan kasar ta Ivory Coast ne dai a ranar 25 ga watan na Oktoba mai zuwa.

Shi dai Alassan Outtara an sake zabarsa shugaban kasa karo na uku  a 2020, alhali tun a baya ya sanar da cewa zai sauka daga kan mukamin nashi.

Outtara ya zama shugaban kasar ta Ivory Coast a karon farko a 2010 a kasar da ita ce mafi girma wajen fitar da Coco a duniya.

Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ya amabto Ottata yana cewa: “Tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar in sake yin hidima a wani jikon, kuma inda da cikakkiyar lafiyar da za ta sa in yi hakan.”

Haka nan kuma ya ce; Ina sake tsaywa takara saboda kasarmu tana fuskantar kalubale mai girma a fagagen tattalin arziki da tsaro da ba a tsaba fuskantar irinsa ba a baya.

 Gabanin zamansa shugaban kasa, Outtara ya kasance kwararre a fagen tattalin arziki wanda ya yi karatunsa a kasar Amurka. Daga cikin ayyukan da ya yi da akwai gwamnan Bankin yammacin Afirka, sannan kuma mataimakin shugaban Asusun Bayar da Lamuni Na Duniya ( IMF).

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran