NAFDAC Ta Rufe Shaguna Da Wuraren Ajiyar Magunguna Marasa Inganci A Legas
Published: 12th, February 2025 GMT
NAFDAC Ta Rufe Shaguna Da Wuraren Ajiyar Magunguna Marasa Inganci A Legas.
এছাড়াও পড়ুন:
Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
Daga Aliyu Muraki
Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta Kasa reshen Jihar Nasarawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya Lafia ta bi umarnin ƙungiyar ta ƙasa wajen shiga yajin aiki na ɗindindin.
Wakilinmu wanda ya ziyarci asibitin koyarwar, ya bayar da rahoton cewa likitocin sun bar wuraren aikinsu domin matsin lamba ga gwamnatin tarayya ta biya dukkan hakkokinsu da ke karuwa zuwa biliyoyin naira.
A yayin ziyarar, ya ruwaito cewa nas nas da ungozoma ne kawai ke kula da marasa lafiya, musamman a sashen bada kulawar gaggawa, inda suke ƙoƙarin taimaka wa waɗanda ke cikin mawuyacin hali, yayin da ake tura waɗanda lamuransu ke neman kulawar likitoci zuwa wasu asibitoci domin samun kulawar gaggawa.
Haka zalika su ma likitocin Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya (FMC) KKeffisun bi sahun takwarorinsu wajen shiga yajin aikin.
Hakan ya tilastawa marasa lafiya barin asibitocin domin komawa asibitoci masu zaman kansu a cikin biranen biyu, yayin da wasu kuma suka koma gida suna jiran tsammani.
A tattaunawa da wasu marasa lafiya, Gloria Namo da Jamil Ishaq, da ke jinya a asibitocin, sun bayyana damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ta kasa biyan bukatun likitocin, wanda hakan ya hana su ci gaba da samun kulawa.
Sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta biyan dukkan haƙƙin likitocin, ganin cewa ba za su iya zuwa asibitoci masu zaman kansu ba saboda tsadar rayuwa.