Leadership News Hausa:
2025-11-03@12:28:09 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

Published: 28th, January 2025 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

“Ƙungiyar Al-Hilal ta gode wa Neymar bisa gudunmuwar da ya bayar, kuma tana masa fatan alheri a nan gaba,” in ji ƙungiyar.

Wannan matakin ya zo ne yayin da ya rage wata bakwai kafin ƙarshen kwantaragin Neymar, wanda ya kai shekara biyu da ƙungiyar.

A Al-Hilal, ana biyan Neymar Yuro miliyan 150 a shekara.

Lokacin da ya koma ƙungiyar, Neymar ya bayyana burinsa na kafa tarihi, amma raunin da ya samu yayin wasan Brazil da Uruguay a shekarar 2023 ya hana shi buga wasanni da dama.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Brazil Neymar Raba Gari Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci

Daga Aliyu Muraki

Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa  ta Kasa reshen Jihar Nasarawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya Lafia ta bi umarnin ƙungiyar ta ƙasa wajen shiga yajin aiki na ɗindindin.

Wakilinmu wanda ya ziyarci asibitin koyarwar, ya bayar da rahoton cewa likitocin sun bar wuraren aikinsu domin matsin lamba ga gwamnatin tarayya ta biya dukkan hakkokinsu da ke karuwa zuwa biliyoyin naira.

A yayin ziyarar, ya ruwaito cewa nas nas da ungozoma ne kawai ke kula da marasa lafiya, musamman a sashen bada kulawar gaggawa,  inda suke ƙoƙarin taimaka wa waɗanda ke cikin mawuyacin hali, yayin da ake tura waɗanda lamuransu ke neman kulawar likitoci zuwa wasu asibitoci domin samun kulawar gaggawa.

Haka zalika su ma likitocin  Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya (FMC) KKeffisun bi sahun takwarorinsu wajen shiga yajin aikin.

Hakan ya tilastawa  marasa lafiya barin asibitocin domin komawa asibitoci masu zaman kansu a cikin biranen biyu, yayin da wasu kuma suka koma gida suna jiran tsammani.

A tattaunawa da wasu marasa lafiya, Gloria Namo da Jamil Ishaq, da ke jinya a asibitocin, sun bayyana damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ta kasa biyan bukatun likitocin, wanda hakan ya hana su ci gaba da samun kulawa.

Sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta biyan dukkan haƙƙin likitocin, ganin cewa ba za su iya zuwa asibitoci masu zaman kansu ba saboda tsadar rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m