Iran Ta Ce Ba Zata Amince Da Barazana Da Kuma Takurawa A Lokaci Guda Da Tattaunawa ba
Published: 2nd, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin JMI ba zata amince da tattaunawa tare da kara tsuge takunkuman tattalin arziki na koli da aka dorawa kasar ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a yau Jumma’a ya kuma kara da cewa yin haka sabawa dokokin kasa da kasa ne.
Kafin haka dai gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan kakabawa mutanen da kamfanoni 7 wadanda suke mu’amala da kasar Iran a kasashen UAE da Turkiya saboda sayan danyen man kasar Iran da kuma sinadaran manfetur na kasar.
Har’ila yau a wani labarin kuma gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan cewa zata kakabawa dukkan kasashen da suke sayen danyen man fetur ko sinadaran manfetur daga kasar Iran nan gaba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya A Matsayar Alamar Yan Ta’adda
Ministan Tsaron kasar Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta zama babbar alamar ta’addanci a duniya
Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh, yayin da yake yin Allah wadai da kisan gillar da yahudawan sahayoniyya suke yi wa al’ummomin Falastinu da na Lebanon a daidai lokacin da kungiyoyin kasa da kasa da tarurrukan kasa da kasa suka yi shiru, yana mai cewa: A yau al’ummar yahudawan sahayoniyya ta zama wata babbar alama ta ta’addancin kasa a duniya.
Birgediya Janar Nasirzadeh ya furta haka ne a ganawarsa da ministan tsaron Jamhuriyar Zimbabwe Uba Muchinguri Kashiri a lokacin ziyararsa a kasar Iran, inda suka tattauna batutuwan da suka shafi kasashen biyu. A cikin wannan ganawar, ministan tsaron na Iran ya jaddada cewa: Dangantakar dake tsakanin Iran da Zimbabwe tana da tushe mai tarihi, kuma ta kasance a ko da yaushe bisa abota da mutunta juna. Ya kara da cewa, a cikin shekarun da suka gabata, kasashen biyu sun sami ci gaba mai kyau a dangantakar dake tsakanin kasashensu.