Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Published: 3rd, May 2025 GMT
Shugaban INEC ya jaddada muhimman ci gaban da ya samo asali daga sauye-sauyen da suka gabata da suka hada da fadada jaddawalin zabe, gyare-gyare don ba da damar kwanaki 180 tsakanin zaben fid da gwani na jam’iyya da zabe daga kwanaki 60 ya warware jinkirin kayan aiki. Ya ce wannan ya tabbatar da cewa an gudanar da babban zaben 2023 ba tare da jinkirta ba, a karon farko tun 2010.
Ya ce wani ci gaba kuma ya hada da samar da kayan aiki na cikin gida, yana mai cewa a karon farko tun 1999, an buga dukkan kayan zabe masu muhimmanci a Nijeriya,
Farfesa Yakubu ya bayyana kalubalen da ke bukatar kulawar majalisa, da suka hada da karfafa goyon bayan doka ga sabbin abubuwa na INEC, kamar tsarin zabe da na’ura, rage shari’a bayyana rikice-rikice a cikin dokokin zabe da amincewa da shawarwarin da aka bayar a baya na gyare-gyare kwamitocin ciki har da Uwais (2009), Lemu (2011), da kuma Nnamani (2017).
Shugaban INEC ya jaddada cewa irin wannan lamari yana ba da gudummawa mai yawa fiye da sauraren kwamitocin da aka saba, wanda ke ba ‘yan majalisa damar samun fahimtar farko game da kalubalen gudanar da zabe. Ya kuma yaba da goyon bayan abokan hulda suke bayarwa wajen habaka zaben Nijeriya.
Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar dinke bakin zaren, INEC na shirin musayar basira tare da ‘yan majalisa don jagorantar wasu gyare-gyare ga kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima da dokar zabe.
A cewar FarfesaYakuba, manufar ita ce karfafa tsarin zaben Nijeriya gabanin zabe na gaba a 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp