Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Published: 3rd, May 2025 GMT
Shugaban INEC ya jaddada muhimman ci gaban da ya samo asali daga sauye-sauyen da suka gabata da suka hada da fadada jaddawalin zabe, gyare-gyare don ba da damar kwanaki 180 tsakanin zaben fid da gwani na jam’iyya da zabe daga kwanaki 60 ya warware jinkirin kayan aiki. Ya ce wannan ya tabbatar da cewa an gudanar da babban zaben 2023 ba tare da jinkirta ba, a karon farko tun 2010.
Ya ce wani ci gaba kuma ya hada da samar da kayan aiki na cikin gida, yana mai cewa a karon farko tun 1999, an buga dukkan kayan zabe masu muhimmanci a Nijeriya,
Farfesa Yakubu ya bayyana kalubalen da ke bukatar kulawar majalisa, da suka hada da karfafa goyon bayan doka ga sabbin abubuwa na INEC, kamar tsarin zabe da na’ura, rage shari’a bayyana rikice-rikice a cikin dokokin zabe da amincewa da shawarwarin da aka bayar a baya na gyare-gyare kwamitocin ciki har da Uwais (2009), Lemu (2011), da kuma Nnamani (2017).
Shugaban INEC ya jaddada cewa irin wannan lamari yana ba da gudummawa mai yawa fiye da sauraren kwamitocin da aka saba, wanda ke ba ‘yan majalisa damar samun fahimtar farko game da kalubalen gudanar da zabe. Ya kuma yaba da goyon bayan abokan hulda suke bayarwa wajen habaka zaben Nijeriya.
Yayin da ake ci gaba da lalubo hanyar dinke bakin zaren, INEC na shirin musayar basira tare da ‘yan majalisa don jagorantar wasu gyare-gyare ga kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima da dokar zabe.
A cewar FarfesaYakuba, manufar ita ce karfafa tsarin zaben Nijeriya gabanin zabe na gaba a 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.
Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.
Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.
Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.
Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.
Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.