Wuta ta tashi da safiyar yau Juma’a inda ta ƙone shaguna uku da wasu kayayyaki masu yawa a unguwar Sango da ke cikin babban birnin jihar Oyo, Ibadan. Manaja Janar na hukumar kashe gobara ta Jihar Oyo, Akinyemi Akinyinka, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa wutar ta tashi a bayan wani gidan man da ke Sango.

Akinyinka ya ce an ba da rahoton faruwar gobarar da karfe 4:41 na safe ta wayar tarho, kuma ma’aikatan hukumar, ƙarƙashin jagorancin ACFS Adedeji (Mrs.), sun isa wurin nan da nan. “Lokacin da muka isa, mun gano cewa shaguna uku daga cikin goma na shagunan sun ƙone. Mun yi sauri mu kawar da wutar kuma mun hana ta yaɗuwa zuwa sauran shaguna,” in ji shi.

Gobara A Haramtacciyar Wurin Ajiye Man Fetur Ta Ci Rayukan Mutane 5 A Jihar Ribas Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

Ko da yake ba a sami rahoton asarar rayuka ba, amma wutar ta lalata shaguna uku, da Firinji, da abubuwan sha. Akinyinka ya bayyana cewa wutar ta fara ne sakamakon wutar da ta fito daga firiji da aka sa a cikin shagon, wanda ya ƙona wasu abubuwa masu saurin kamawa kafin ya mamaye shagunan.

Ma’aikatan kashe gobara sun ceci wasu shaguna da kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin Naira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

Bayan gobarar, jami’an kashe gobara sun kai ɗauki, kuma sun samu nasarar kashe wutar.

A shekarar 2014, ƙungiyar Boko Haram ta kai wa wannan bariki na Giwa hari, inda ta kashe mutane da dama tare da jikkata wasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarki Sanusi ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4
  • Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024
  • NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
  • Zamfara Ta Biya Sama Da Naira Biliyan 13 A Matsayin Bashin Garatuti Da Aka Gada – Mataimakin Gwamna.
  • Masifar Gobara Tana Kara Bunkasa A Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tare Da Fara Raba Yahudawa Da Muhallinsu
  • Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara
  • Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna