Leadership News Hausa:
2025-08-01@22:18:09 GMT

Hanyoyin Warware Matsalolin Ma’aurata(1)

Published: 6th, April 2025 GMT

Hanyoyin Warware Matsalolin Ma’aurata(1)

Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam’iyyar APC  Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

Maimakon mu guje wa matsalolin da muke fuskanta, ya kamata mu nemi shawarar magance su. Idan kuka bi ka’idodin hakan zai taimaka muku ku magance matsalolinku.

Ku tattauna matsala:

Akwai lokacin magana, Ku tabbata cewa kun tattauna matsalar sosai.

Ka gaya wa matarka ainihin abin da ke zuciyarka da kuma ra’ayinka a kan batun. A kowane lokaci, ku gaya wa junanku gaskiya, ko da abin vacin rai ya faru kada ku yi fada. Idan ka yi maganar da za ta sanyaya zuciyar matarka ba za ku yi gardama ba.

Ko da ba ku jitu a kan wannan batu ba ku ci gaba da yi wa juna alheri da kyakkyawan zato, kada ku manta cewa ya kamata ku rika nuna wa juna kauna da ban girma, ku yi kokari ku sasanta matsalar da ke tsakaninku nan da nan, kuma kada ku ki yin magana da juna.

Shawara:

Ku keve lokaci don tattauna matsalar da ke tsakaninku, idan matarka tana magana, ka yi kokari ka kyale ta ta gama magana, idan ta gama, sai ka yi magana, ku saurara kuma ku fahimta

Ku kaunaci juna wajen ba da girma, kowa ya riga ba dan’uwansa.

Yana da muhimmanci ka kasa kunne da kyau sa’ad da matarka take magana, ka yi kokari ka fahimci ra’ayinta kuma ka yi hakan da juyayi da kuma tawali’u. Kada ka yi kamar kana saurara kawai, idan da hali ka bar abin da kake yi gabaki daya don ka saurari matarka sosai ko kuma ka tambaye ta ko za ku iya tattauna batun a wani lokaci. Idan kuka dauki juna a matsayin abokai maimakon abokan gaba, ba za ku yi garajen yin fushi ba.

Ko da abin da matarka take fada yana ci maka rai, ka ci gaba da saurarawa don ka fahimce ta ka mai da hankali ga abin da take nufi maimakon kalmomin da take furtawa. Ka lura da muryarta da kuma fuskarta yayin da take magana.

A cikin dukan aiki akwai riba, amma tadin baki ba ya nufa ko ina sai wajen tsiya, yanke shawara mai kyau kawai ba shi ne aikin ba. Kuna bukatar ku yi abin da kuka shawarta za ku yi, yin hakan ba zai kasance da sauki ba, amma za ku samu sakamako mai kyau. Idan kuka ba juna hadin kai, za ku girbi ‘amfanin wahalarku.

Kowannenku ya Kudura yin abin da zai iya yi don ku warware matsalar da ke tsakaninku a lokaci-lokaci, ku zauna ku bincika don ku ga ko kuna samun ci gaba a wannan batun.

Idan kai da matarka kuka yi kokari sosai, aurenku zai yi dadi maimakon daci. Kada ku ta da maganar da ta riga ta mutu, ku mai da hankali ga na gaba, idan kuka ba wa juna hadin kai kuma kuka bi ka’ida za ku iya warware duk wata matsala da ta kunno kai.Ka tambayi kanka.

Wace matsala ce nake bukatar tattaunawa da matata cikin gaggawa?

Me zai taimaka mini in fahimci ra’ayin matata a kan wannan batun?

To daga nan kun san abin da ya kamata ku yi, sai ku dau himma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

Ya nuna rashin jin daɗinsa da rabon ayyukan tituna kamar yadda aka samu a cikin wata sanarwa da ma’aikatar ayyuka ta fitar a watan Mayun 2025, wanda a cewarsa, an ware Naira tiriliyan 1.394 wa yankin Kudu-maso-Yamma, yayin da ɗaukacin yankin Arewa-maso-gabas suka samu Naira biliyan 30, sai kuma yankin Arewa-maso-Yamma Naira 105 biliyan.

“Rashin tsaro ya zama babban abin damuwa, ƴan fashi, tada ƙayar baya, da kuma garkuwa da mutane na ci gaba da wanzuwa a sassan Arewa da dama, inda jihohi kaɗan ne kamar Kaduna da Bauchi suka samu kwanciyar hankali,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta fito da manufofin siyasa don kawo ƙarshen rikicin.

ɗalhatu ya kuma soki manufofin gwamnatin tarayya kan harkokin noma, inda ya ce sun jawo ce-ce-ku-ce a harkar noma a cikin gida, sakamakon ƙaruwar shigo da abinci daga ƙasashen waje, lamarin da ya sa aka rufe wasu masana’antun shinkafa a yankin. Ya yi gargaɗin cewa irin waɗannan manufofin suna raunana ƙashin bayan tattalin arzikin yankin.

Ya ƙara da nuna damuwa game da giɓin da ake samu na wutar lantarki a yankin, ya kuma buƙaci shugaba Tinubu ya kafa dokar ta-ɓaci a fannin wutar lantarki. Ya buƙaci a gaggauta kammala wasu muhimman ayyukan makamashi kamar madatsar ruwa ta Mambilla da bututun iskar gas daga Abuja zuwa Kaduna da Kano, waɗanda a cewarsa, suna da matuƙar muhimmanci ga makomar masana’antun Arewacin Nijeriya.

A ɓangaren ilimi kuwa, ɗalhatu ya buga misali da bayanan bankin duniya da ke nuni da cewa kashi 80 cikin 100 na yara miliyan 20 na Nijeriya da aka ƙiyasta ba sa zuwa makaranta ƴan Arewa ne. Ya buƙaci gwamnatin Tinubu da ta sake ƙaddamar da shirin ilimi na bai ɗaya (UBE) tare da himma wajen da mai da hankali kan ilimi kyauta.

Ya kuma yi tir da taɓarɓarewar ababen more rayuwa na kiwon lafiyar al’umma, da sake ɓullar cututtuka, da yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasan Arewa, inda ya yi kira da a gaggauta ɗaukar matakin na gwamnatin tarayya a fannonin kiwon lafiya na matakin farko, da sarrafa magunguna, da samar da ruwan sha.

Ya bayyana tafiyar hawainiyar da ake yi a kan aikin kamfanin tama da ƙarafa na Ajaokuta a matsayin abin takaici, ya kuma yi gargaɗin a kan dogaro da ƙawancen jama’a da masu zaman kansu (PPP) fiye da kima wajen samar da irin waɗannan kadarorin.

ɗalhatu ya zargi gwamnatin Tinubu da nuna ɓangaranci, son zuciya, da rashin sanin halin da Arewa ke ciki.

Hausawa na Karin magana cewa “Gyara kayanka ba ya zama sauke mu raba,”. Ya ba da shawarar sake farfaɗo da kwamitin tuntuɓar gwamnatin tarayya domin zurfafa tattaunawa.

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, Shugaban ƙungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce Shugaba Tinubu ya cika alƙawuran da ya ɗaukar wa Arewa kuma yana ci gaba da aiwatar da ajandarsa ta ‘Renewed Hope’

Gwamna Yahaya ya ce tarurrukan da suka haɗa da ƙungiyar SABMF na da matuɗar muhimmanci wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da tabbatar da bin doka da oda, amma ya jaddada cewa shaidun da ke ƙasa na nuna ci gaba mai ma’ana a sassa daban-daban na faɗin yankin.

“Lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya yi yaƙin neman zaɓe a faɗin Arewa a shekarar 2023, ya yi alƙawuran da ya dace, a yau muna ganin cikarsu ta hanyar ayyukan da aka kammala da kuma waɗanda ke ci gaba da gudana,” in ji Yahaya, inda ya ƙara da cewa an samu gagarumin ci gaba a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano, layin dogo na Kano-Katsina-Maradi, gyaran matatar mai ta Kaduna, da kuma bunƙasa man fetur na Kolmani.

Yahaya lauded the newly established Ministry of Liɓestock ɗeɓelopment, calling it a major step towards modernising pastoral systems in the region.

Ya kuma bayyana cewa an samu ci gaba a harkokin tsaro a jihohi da dama, inda ya yi nuni da yadda aka kawar da shugabannin ta’addanci da ƴan fashi sama da 300.

Yahaya ya yaba wa sabuwar ma’aikatar kula da kiwon dabbobi da aka kafa, inda ya bayyana hakan a matsayin wani babban mataki na zamanantar da tsarin kiwo a yankin.

A cewarsa, sabbin ababen more rayuwa na tituna da na dogo, inganta kiwon lafiya, ayyukan noma, da kuma ɗaukar matakan da suka dace a fannin ilimi, musamman kan matsalar Almajirai da yaran da ba su zuwa makaranta, na nuni da dabarun da gwamnatin tarayya ta yi domin ɗaukaka yankin.

A nasa jawabin, Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya wakilci Shugaba Tinubu, ya nanata ƙudurin Shugaban ƙasa na samar da ci gaba mai amfani, yana mai bayyana cewa “ba wani yanki da za a barI baya.

Akume, wanda ya jagoranci tawagar ministoci, shugabannin hukumomi, da mataimakan shugaban ƙasa a wajen taron, ya ce ajandar Renewed Hope an kafa ta ne a kan ginshiƙan daidaito, shiga tsakani, da kuma gaskiya.

Ya zayyana muhimman ayyukan da ake gudanarwa a Arewa da ma faɗin ƙasar nan.

Ya ambaci babbar hanyar Legas zuwa Calabar, babbar titin Sokoto-Badagry, Kano-Maradi da Fatakwal-Maiduguri, da ayyukan gina gidaje da na noma da dama a matsayin shaida na ayyukan gwamnati.

Akan sake fasalin tattalin arziki, Akume ya ce cire tallafin man fetur da kuma haɗewar farashin canji abu ne mai zafi amma an yi su a matakan da suka dace domin daidaita tattalin arzikin ƙasar.

Ya bayyana cewa an riga an bayar da sama da Naira biliyan 53 ta tsarin bayar da lamunin rancen ɗalibai don cin gajiyar ɗaliban manyan makarantu sama da 400,000 a faɗin ƙasar nan.

Akume ya ce Tinubu ya ɗau turbar kai Nijeriya matsayin da ya yi alƙawri, inda ya ƙara da cewa.

“Zan buƙaci ƴan siyasa daga yankin Arewa da su jira har zuwa 2031. Kada ku shiga ƙungiyar da za ta haifar da lalata ci gaba daban-daban da Shugaba Tinubu ya samu. Shugaban ƙasa ya taɓa dukkan sassan ƙasar nan da kowane ɗan ƙasa.”

Ya kuma jinjinawa marigayi Firimiyan Arewacin NIjeriya, Sir Ahmadu Bello, inda ya bayyana shi a matsayin ɗan siyasa mai wakiltar haɗin kai, hangen nesa, da gudanar da mulki na bai ɗaya. Ya kuma yaba da gudunmawar da wasu fitattun shugabannin Arewa suka bayar da suka haɗa da Cif Solomon Lar da Malam Adamu Ciroma.

Waɗanda suka yi wa ƙasa hidima da tsaffin gwamnonin Arewa, ministoci, masu ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA) Malam Nuhu Ribadu, Shugaban ma’aikatan Fadar Shugaban ƙasa Sanata George Akume, shugabannin gargajiya, shugabannin MɗA na tarayya, shugabannin tsaro, da shugabannin masana’antu ne suka hallarci taron.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  
  • Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya