Aminiya:
2025-08-02@05:00:15 GMT

Yadda aka yi jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi a Bauchi

Published: 4th, April 2025 GMT

Dubban mutane ne suka halarci jana’izar shahararren malamin addinin Musuluncin nan kuma Babban Limamin Masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, Sheikh Dokta Idris Abdulaziz.

Malamin ya rasu ne a ranar Alhamis a gidansa da ke Bauchi bayan fama da doguwar rashin lafiya.

Kotun ƙoli ta sauke Julius Abure daga shugabancin jam’iyyar LP Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike

Ya je ƙasashen Masar da Saudiyya domin neman magani kafin watan Ramadan.

Tun da safiyar ranar Juma’a, ɗaruruwan ɗalibansa da mabiyansa daga Bauchi, maƙwabtan garuruwa da kuma wasu jihohi sun taru a gidansa domin halartar jana’izarsa.

An gudanar da sallar jana’izar a ranar Juma’a a filin Idi na Games Village.

Manyan malamai, ’yan siyasa, ’yan uwa da abokan arziƙi da kuma mazauna birnin Bauchi sun halarci jana’izar.

Aminiya ta ruwaito cewar lokaci na ƙarshe da aka gan shi a bainar jama’a shi ne a ranar Sallah, inda ya yi wa al’ummar Musulmi jawabi bayan sallar Idi, inda ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da juna.

Ga hotunan yadda jana’izar ta gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rashin lafiya rasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su, bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin sun yi garkuwa da su a wani mummunan musayar wuta da aka yi a tsaunin Shanga.

Waɗanda aka yi garkuwan da su sun haɗa da: Muhammad Nasamu Namata mai shekara 25, da Gide Namata mai shekara 20 da Hamidu Alhaji Namani mai shekara 35.

INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi

An  yin garkuwa da su ne a safiyar ranar 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da masu garkuwa da mutane ɗauke da makamai suka mamaye ƙauyen Sangara da ke Ƙaramar hukumar Shanga.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa wannan ceton ya biyo bayan ɗaukar matakin gaggawa da jami’an ’yan sanda na yankin Shanga suka ɗauka, wanda ya haɗa tawagar jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an sojojin Najeriya, jami’an tsaro na Civil Defence da ’yan banga na yankin da mafarauta.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ta bi sahun masu garkuwa da mutanen ne zuwa tsaunin Shanga, inda aka yi musayar wuta a tsakaninsu, musayar wutar ta sa jami’an tsaro suka yi nasara kan masu garkuwar.

Daga nan masu garkuwan suka tsere zuwa cikin daji da raunukan harbin bindiga.

“An kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su ne ba tare da wani rauni ba, a ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025 da misalin ƙarfe 3:30 na rana kuma a halin yanzu suna samun kulawar likita kafin su sake haɗuwa da iyalansu.”

Ya ce, Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello M. Sani ya yaba wa jarumtaka da ƙwarewa na rundunar, inda ya buƙaci dukkan hukumomin tsaro su ci gaba da haɗa kai. Ya nanata ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi a Jihar Kebbi.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da kai rahoto ga jami’an tsaro mafi kusa domin ɗaukar matakin gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta
  • GORON JUMA’A 01-07-2025
  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina