Yadda yi jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi a Bauchi
Published: 4th, April 2025 GMT
Dubban mutane ne suka halarci jana’izar shahararren malamin addinin Musuluncin nan kuma Babban Limamin Masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, Sheikh Dokta Idris Abdulaziz.
Malamin ya rasu ne a ranar Alhamis a gidansa da ke Bauchi bayan fama da doguwar rashin lafiya.
Kotun ƙoli ta sauke Julius Abure daga shugabancin jam’iyyar LP Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — WikeYa je ƙasashen Masar da Saudiyya domin neman magani kafin watan Ramadan.
Tun da safiyar ranar Juma’a, ɗaruruwan ɗalibansa da mabiyansa daga Bauchi, maƙwabtan garuruwa da kuma wasu jihohi sun taru a gidansa domin halartar jana’izarsa.
An gudanar da sallar jana’izar a ranar Juma’a a filin Idi na Games Village.
Manyan malamai, ’yan siyasa, ’yan uwa da abokan arziƙi da kuma mazauna birnin Bauchi sun halarci jana’izar.
Aminiya ta ruwaito cewar lokaci na ƙarshe da aka gan shi a bainar jama’a shi ne a ranar Sallah, inda ya yi wa al’ummar Musulmi jawabi bayan sallar Idi, inda ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da juna.
Ga hotunan yadda jana’izar ta gudana:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rashin lafiya rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA