Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
Published: 1st, March 2025 GMT
Shugabannin kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombia sun jaddada aniyarsu ta hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila amfani da tashar jiragen ruwansu, a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi a zirin Gaza.
“Za mu hana jiragen ruwa da ke dauke da kayan aikin soji zuwa Isra’ila amfani da tashoshin jiragen ruwanmu; kamar yadda,” Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, Firayim Ministan Malaysia Anwar Ibrahim da Shugaban Colombia Gustavo Petro suka rubuta a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da mujallar harkokin waje ta buga a wannan makon.
Sun jaddada cewa yakin da Isra’ila ke yi a Gaza ya fallasa gazawar tsarin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen rashin hukunta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi.
Malesiya da Colombia na daga cikin kasashen da suka goyi bayan korafin kisan kiyashin da kasar Afrika ta kudu ta kai kan Isra’ila a kotun duniya ta ICJ.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.
Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.
Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin TarayyaAn kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.
A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.
Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.
Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.
Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.
Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.
A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.
Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.
“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.
Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.
Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.
“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.