Aminiya:
2025-07-31@14:06:48 GMT

Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi cikin ta lalata wani ɓangare na Asibitin Ago da ke kan titin Ago Palace, Okota, a Jihar Legas.

Gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Juma’a, inda ta shafi wani sashe na ginin mai bene hawa ɗaya, inda asibitin yake.

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Likitoci da marasa lafiya da ke cikin asibitin sun tsere domin tsira da rayukansu yayin da wutar ta bazu.

Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Lagos (LASEMA), Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce jami’ansu sun isa wajen gobarar da misalin ƙarfe 8:45 na dare.

Binciken da LASEMA ta gudanar ya nuna cewa gobarar ta faru ne sakamakon matsalar wutar lantarki.

Rahotanni sun nuna cewar babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata.

Jami’an kashe gobara daga LASEMA da LRU da sauran masu bayar da agajin gaggawa sun haɗa kai don shawo kan gobarar tare da hana ta bazuwa zuwa wasu gine-gine da ke kusa da asibitin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai

Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.

A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.

Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14