Aminiya:
2025-04-30@23:30:21 GMT

Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas

Published: 1st, March 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi cikin ta lalata wani ɓangare na Asibitin Ago da ke kan titin Ago Palace, Okota, a Jihar Legas.

Gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Juma’a, inda ta shafi wani sashe na ginin mai bene hawa ɗaya, inda asibitin yake.

Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Likitoci da marasa lafiya da ke cikin asibitin sun tsere domin tsira da rayukansu yayin da wutar ta bazu.

Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Lagos (LASEMA), Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce jami’ansu sun isa wajen gobarar da misalin ƙarfe 8:45 na dare.

Binciken da LASEMA ta gudanar ya nuna cewa gobarar ta faru ne sakamakon matsalar wutar lantarki.

Rahotanni sun nuna cewar babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata.

Jami’an kashe gobara daga LASEMA da LRU da sauran masu bayar da agajin gaggawa sun haɗa kai don shawo kan gobarar tare da hana ta bazuwa zuwa wasu gine-gine da ke kusa da asibitin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine

Fadar Kremlin ta kasar Rasha ta ayyana tsagaita wuta na kwana biyu ita kaɗai a yakinta da kasar Ukraine.

Shugaba Vladimir Putin ya sanar a ranar Litinin cewa Rasha za ta aiwatar da tsagaita wutar ne daga tsakar dare na 8 ga Mayu zuwa tsakar dare na 10 ga Mayu.

A ranakun da za a tsagaita wutar ne Rasha ke bikin karshen da yakinta da kasar Jamus a shekarun 1941 zuwa 1945, wanda aka fi sani da Yakin Duniya na Biyu a yawancin duniya.

A Rasha ana kiran yakin na Duniya na biyu da sunan Babban Yaƙin Ceton Kasa.

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine