Aminiya:
2025-07-31@13:45:19 GMT

HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato

Published: 1st, March 2025 GMT

Ana fargabar cewa wata gobara ta laƙume aƙalla shaguna 100 a Kasuwar Kara da ke Jihar Sakkwato.

Gobarar wadda ta tashi tun da Asubahin wannan Asabar ɗin ta shafe sa’o’i 9 tana ta’adi.

An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa

Wani ɗan kasuwar da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce tun da misalin ƙarfe 6:30 amma sai wurin ƙarfe 3:30 na rana aka samu nasarar kashe ta.

A cewarsa, gobarar ta yi ta’adi a ɓangaren shagunan masu sayar da abinci da suka haɗa da gero, dawa da masara da shinkafa.

Haka kuma, majiyar ta ce wutar ta yi ɓarna a ɓangaren masu ƙyamare da layin maƙera da masu maganin gargajiya.

“A ƙiyasi an yi asarar kuɗi za su kai Naira miliyan 500 domin dukkan shagunan da gobarar ta taɓa sun ƙone ƙurmus, masallaci ne kawai abun bai shafa ba.”

Ya buƙaci gwamnati da ta jingine batun siyasa a gefe wajen kafa kwamitocin da take ɗora wa alhakin bibiyar wannan ibtila’i domin ɗaukar matakan da suka dace bisa adalci.

Ya bayyana cewa wannan shi ne karo na uku cikin ƙasa da shekara ɗaya da ake samun tashin gobara a kasuwar.

Ya nanata kiran cewa bayan jajanta wa ’yan kasuwa akwai kuma buƙatar gwamnati ta ɗauki matakin kare dukiyar mutane daga irin wannan hasara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Jihar Sakkwato Kasuwar Kara

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya

Jamhuriyar Nijar da ƙasar Rasha a ranar Litinin, 28 ga watan Yulin 2025 sun ƙulla yarjejeniya game da makamashin nukiliya da kuma haƙar yuraniyom.

Kamfanin dillancin labaran Nijar (ANP) ya ruwaito cewa ƙasashen biyu sun rattaba hannu a kan yarjejeniyar ce bayan ganawar shugaban Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, da wata babbar tawagar Rasha ƙarƙashin jagorancin Ministan Makamashi, Mista Sergei Tsivilev.

Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma

“Muhimmiyar manufarmu ita ce mu ƙara inganta rayuwar mutanen Nijar da na Rasha,” in ji Sergei, kana ya bayyana cewa sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya game da makamashin nukiliya da haƙar yuraniyom.

“Mun amince cewa za mu horar da manyan jami’ai waɗanda za su iya aiki a fannonin tallafinmu irin na makamashi da noma da lafiya da ilimi, kuma za mu horar da injiniyoyi tun a makarantu domin su ci gaba da karatunsu a jami’o’in da ke Tarayyar Rasha,” in ji shi.

Ganawar ta mayar da hankali ne kan dangantaka tsakanin Tarayyar Rasha da Nijar, in ji rahoton na ANP.

Bayan ganawar dai Ministan na Rasha ya bayyana godiyarsa ga shugaba da mutanen Nijar domin irin tarbar da aka yi masa.

“Mun ga bayanai da dama game da damarmakin da ke akwai a cikin Nijar, kuma a halin yanzu mutanenmu na ƙoƙarin aiki kan damarmakin da ke nan a Nijar,” in ji Mista Sergei Tsivilev, wanda shi ne shugaban ɓangaren Rasha a hukumar haɗakar gwamnatoci da ƙasashen AES.

“Shugaban ƙasar ya kuma sanar da mu cewa shi zai zaɓi shugaba na ɓangare ɗaya na hukumar haɗakar gwamnatocin nan ba da jimawa ba domin ayyukanmu da ‘yan uwanmu na Nijar su yi ta tafiya babu tangarɗa,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano