HausaTv:
2025-08-02@00:54:26 GMT

 Sojojin Sudan Sun Kwance Iko Da Garin “Khartum-al-Bahri”

Published: 29th, January 2025 GMT

A yau Laraba ne dai sojojin Sudan su ka sanar da shimfida ikonsu a garin ‘Khartum-al-Bahri.

Majiyar sojan kasar ta Sudan ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu suna aiki tare da bangarorin da suke dace, domin ganin fararen hula mazauna garin sun koma gidajensu a cikin lokaci mafi kusa.

A cikin kwanaki kadan da su ka gabata sojojin na kasar Sudan sun sami nasarar kwace yankuna da dama a kewayen Khartum-al-Bahri da su ka hada da gabashin tekun maliya.

Wannan cigaban da sojojin na Sudan su ka samu, ya biyo bayan korar dakarun rundunar kai daukin gaggawa ne daga babbar shalkwatar soja dake tsakiyar birnin Khartum, haka nan kuma cibiyar sojan ta sadarwa, da babbar cibiyar leken asiri ta soja dake kusa da Khartum-al-Bahri.

 A wata sanawar ta daban da sojojin kasar ta Sudan su ka fitar sun bayyana cewa jiragen yaki sun kai hare-hare a garin al-Fashar da can ne babban birnin yankin Darfur. Wannan yankin shi ne babban sansanin mayakan dakarun rundunar kai daukin gaggawa.

Sojojin na Sudan sun ce, sun kai wadannan hare-haren ne dai da safiyar Yau Laraba.

A wani labarin daga Sudan, rundunar kai daukin gaggawa ta sanar da cewa, an kashe daga cikin kwamandojinta mai suna Rahmatullah al-Mahadi wanda aka fi sani da Jalha a jiya Talata, ba tare da bayyana yadda aka kashe shi din ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Khartum al Bahri

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta a Ƙaramar Hukumar Yauri ta Jihar Kebbi a wani mataki don bunƙasa harkokin tsaron iyakokin ruwa.

Hakan na zuwa ne bayan da wata tawagar manyan jami’an sojojin ruwan suka kai ziyara gidan gwamnatin Jihar Kebbi.

Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta  ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa

Sojojin sun kai ziayarar ne ƙarƙashin jagorancin Rear Admiral Patrick Nwatu – wanda ya wakilci babban hafsan sojin ruwan ƙasar.

Rundunar ta ziyarci Kebbi ne domin duba yadda za ta samar da sansaninta a jihar.

Patrick Nwatu ya yi tir da harin ta’addanci a kogin Neja, yana mai cewa yankin ya zama maɓoyar masu safarar makamai da sauran masu aikata laifuka.

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ce ta kammala shirye-shiryen kafa sansanin sojin ruwa a garin Yauri da ke jihar.

Babban Hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla ne ya bayyana hakan a wata ziyarar ban girma da suka kaiwa Gwamnan Kebbi, Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

Da yake jawabi yayin ziyarar, jagoran tawagar Rear Admiral Patrick Nwatu, ya ce ziyarar wani ɓangare ne na faɗaɗa dabarun teku na sojojin ruwan Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi
  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  • Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan
  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami