Sojojin Sudan Sun Kwance Iko Da Garin “Khartum-al-Bahri”
Published: 29th, January 2025 GMT
A yau Laraba ne dai sojojin Sudan su ka sanar da shimfida ikonsu a garin ‘Khartum-al-Bahri.
Majiyar sojan kasar ta Sudan ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu suna aiki tare da bangarorin da suke dace, domin ganin fararen hula mazauna garin sun koma gidajensu a cikin lokaci mafi kusa.
A cikin kwanaki kadan da su ka gabata sojojin na kasar Sudan sun sami nasarar kwace yankuna da dama a kewayen Khartum-al-Bahri da su ka hada da gabashin tekun maliya.
Wannan cigaban da sojojin na Sudan su ka samu, ya biyo bayan korar dakarun rundunar kai daukin gaggawa ne daga babbar shalkwatar soja dake tsakiyar birnin Khartum, haka nan kuma cibiyar sojan ta sadarwa, da babbar cibiyar leken asiri ta soja dake kusa da Khartum-al-Bahri.
A wata sanawar ta daban da sojojin kasar ta Sudan su ka fitar sun bayyana cewa jiragen yaki sun kai hare-hare a garin al-Fashar da can ne babban birnin yankin Darfur. Wannan yankin shi ne babban sansanin mayakan dakarun rundunar kai daukin gaggawa.
Sojojin na Sudan sun ce, sun kai wadannan hare-haren ne dai da safiyar Yau Laraba.
A wani labarin daga Sudan, rundunar kai daukin gaggawa ta sanar da cewa, an kashe daga cikin kwamandojinta mai suna Rahmatullah al-Mahadi wanda aka fi sani da Jalha a jiya Talata, ba tare da bayyana yadda aka kashe shi din ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Khartum al Bahri
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.
Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.
An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.
“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.
Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.
Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.
Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.
An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.
Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.