HausaTv:
2025-05-01@06:20:02 GMT

 Sojojin Sudan Sun Kwance Iko Da Garin “Khartum-al-Bahri”

Published: 29th, January 2025 GMT

A yau Laraba ne dai sojojin Sudan su ka sanar da shimfida ikonsu a garin ‘Khartum-al-Bahri.

Majiyar sojan kasar ta Sudan ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu suna aiki tare da bangarorin da suke dace, domin ganin fararen hula mazauna garin sun koma gidajensu a cikin lokaci mafi kusa.

A cikin kwanaki kadan da su ka gabata sojojin na kasar Sudan sun sami nasarar kwace yankuna da dama a kewayen Khartum-al-Bahri da su ka hada da gabashin tekun maliya.

Wannan cigaban da sojojin na Sudan su ka samu, ya biyo bayan korar dakarun rundunar kai daukin gaggawa ne daga babbar shalkwatar soja dake tsakiyar birnin Khartum, haka nan kuma cibiyar sojan ta sadarwa, da babbar cibiyar leken asiri ta soja dake kusa da Khartum-al-Bahri.

 A wata sanawar ta daban da sojojin kasar ta Sudan su ka fitar sun bayyana cewa jiragen yaki sun kai hare-hare a garin al-Fashar da can ne babban birnin yankin Darfur. Wannan yankin shi ne babban sansanin mayakan dakarun rundunar kai daukin gaggawa.

Sojojin na Sudan sun ce, sun kai wadannan hare-haren ne dai da safiyar Yau Laraba.

A wani labarin daga Sudan, rundunar kai daukin gaggawa ta sanar da cewa, an kashe daga cikin kwamandojinta mai suna Rahmatullah al-Mahadi wanda aka fi sani da Jalha a jiya Talata, ba tare da bayyana yadda aka kashe shi din ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Khartum al Bahri

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72

Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Bangaren Guda kuma na sa’o’ii 72 ko kwanaki 3, daga 8-10 na watan Mayu mai zuwa.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya nakalto jakadan kasar Rasha a Abuja yana fadar haka a wani taro baje kolin hotinan yaki Rasah da Nazi a dai dai lokacinda kasar take cikar shekaru 80 da samun nasara a kan sojojin Nazi a karshen yakin duniya na II a Abuja.

Andrey Podelyshev yace idan kasar Ukraine ta zami da tsagaita wuta a cikin wadannan kwanaki ba laifi, amma kuma idan sojojinta sun kai wani hari a kan rasha ta zata rama da hare-hare masu tsanani.

Shugaban Volodimir Zelesky dai tuni ya yi watsi da tsagaita wutar ya kura kara da cewa Rasha tana son ta ja hankalin duniya ne da wannan tsagaita wuta, don amfanin kanta a yakin da suke fafatawa. A halin yanzu dai an dai kwanaki kimani 1,159 aka fafatawa tsakanin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72