Tinubu zai yi shekara takwas yana mulki – Afenifere
Published: 2nd, May 2025 GMT
Ƙungiyar Yarabawa zalla ta Afenifere, ta shaida wa masu sukar Shugaba Bola Tinubu cewa zai yi wa’adi biyu ne a kan karagar mulki.
Kungiyar ta kuma ce rashin adalci ne a hana Tinubu ya sake tsayawa takara a zaɓen 2027, ganin cewa jigo a Arewa, tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, a baya ya yi cikakken wa’adi biyu a ofishi shugaban ƙasa.
Afenifere ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da sakataren ƙungiyar ta ƙasa Kole Omololu ya sanarwa manema labarai a ranar Juma’a, wadda Daily Trust ta samu.
“An bar Buhari ya cika aikin da aka ba shi. Irin wannan ƙa’ida ta adalci da ci gaba dole ne a yi aiki da ita a yanzu. Kada kowa ya nemi a hana yin adalci ga wani a lokacin da ya dace da shi, amma a lokacin da ya dace ake son hana wasu.
“Shugaba Tinubu zai cika wa’adinsa na shekaru takwas, bisa ga ra’ayin mutanen kirki na ƙasar nan, kuma a ƙarƙashin tsarin mulkin ƙasa. Ba da shawarar hana hakan yin watsi ne ga tsarin ƙasar,” in ji kungiyar.
A yayin da Kungiyar ke yabawa gwamnatin shugaba Tinubu kan kawo sauyi a ƙasar, Ƙungiyar Afenifere ta kuma buƙaci masu sukar shugaban da su daina bayyana gwamnati a matsayin gwamnatin da Yarbawa ke jagoranta.
Kungiyar ta lura cewa rashin gaskiya ne a yi wa gwamnatin Tinubu laƙabi da ƙabilanci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Muhammadu Buhari
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran
Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.
Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.
Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.