Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina
Published: 2nd, May 2025 GMT
A yau Juma’a 2 ga watan Mayu, 2025 Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ke ziyartar Jihar Katsina a karon farko tun bayan hawansa kujerar mulki.
Kamar yadda gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa ta ce, shugaban zai duba wasu muhimman ayyukan da gwamnan ya aiwatar da waɗanda ake cikin yi.
Wakilin mu ya tuntuɓi wasu daga cikin al’ummar jihar domin jin ra’ayoyinsu akan wannan ziyara.
Ya zo ɗaurin auren ’yar gwamna ne — Sabo Musa
Alhaji Sabo Musa shi ne mai bai wa Gwamna Raɗɗa shawara a kan wayar da kan al’umma a harkokin gwamnati, ya bayyanawa wakilinmu cewar, Shugaba Tinubu zai zo Katsina ne domin halartar ɗaurin auren ’yar Gwamna Raɗɗa wanda za a yi a ranar Asabar, 3 ga watan Mayu, 2025.
Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan Legas Gobarar rumbum makamai Maiduguri da Matakan da ya kamata a ɗauka — ƘwararruAkan haka ne aka yi amfani da wannan dama wajen gayyatar shi da ya ƙaddamar da wasu ayyukan da Gwamna Raɗɗa ya aiwatar da waɗanda ake cikin yi.
“Ai ka ga mu a yanzu sai mu ce wani abin alfahari ne ga jama’ar Jihar Katsina domin tun hawan shi mulki ita ce jiha ta farko da ya fara zuwa a Arewa inda ya amsa goron gayyata. Shi ya sa aka yi amfani da damar domin ya ziyarci wuraren da shi Gwamna ya aiwatar da kuma inda ake cikin aiwatar da wasu muhimman aiyuka.”
“A kan haka ma har shi Gwamna ya ba mutanen da ke kusa da masallacin da za a yi wannan ɗaurin aure haƙuri a kan ɗan ƙuncin da za su gani a wannan lokacin. Sannan ya yi kira ga al’umma da su fito domin tarbar shugaban kamar yadda aka san Katsina ɗakin kara ce”, in ji Sabo Musa.
Mun yi zaton ziyarar aiki ce kawai
Mafi yawan mutanen da muka tuntuɓa a kan wannan ziyara sun ce sun yi zaton ziyarar aiki ce.
Malam Halliru ya ce, “farko na yi zaton zai zo duba aikin hanyar da ta tashi daga Katsina zuwa Kano ce da aikin ya tsaya, da kuma batun wutar lantarki mai aiki da iska ta hanyar Rimi wadda ita ma ta yi tsaye cik.
Amma sai kawai na ji an ce, zai zo wajen ɗaurin auren ɗiyar Gwamna ne. Ke nan, babu wani abin a zo a gani da za mu ce na Gwamnatin Tarayya ne wanda ya zo a kan shi”.
Shi kuwa Abu Ƙasim cewa ya yi, ko ba komai a iya cewa jihar ta kafa tarihi daga cikin jihohin Arewa domin a nan zai fara kawo ziyarar yini biyu.
“Ina kyautata zaton cewa, a wannan ɗan lokacin ba zai rasa ganin wasu daga cikin dattawan jihar ba, inda za su bayyana mashi wasu abubuwan da jahar take ciki musamman batun matsalar tsaron da ta addabe mu. Sannan tunda inda zai je wajen duba aikin waccan hanya da aka yi magana wurin da wannan hanyar da aka yi watsi da aikin ta ne, Katsina zuwa Kano, zai ga irin halin da ake ciki da kuma irin ayyukan da shi Gwamna ke yi wanda ko makamantan su ita gwamnatin ta Tarayya ba ta yi su ba.
“Ka ga akwai maganar aikin hanyar jirgin ƙasan da ake cewa wai an dakatar, nan ma ina zaton jama’a za su san irin halin da ake ciki. Na kuma san ƙila zai ɗan yi jawabi a wajen buɗe wancan aiki, ƙila ya faɗi wani abu mai muhimmanci da jahar zata amfana.”
Malama Rabi, wata mai sayar da abinci, ta ce, “ni ina zaton samun abokan ciniki kawai saboda shigowar baƙi, amma in baya ga haka sai in ce banga tasirin wannan ziyara ba. Shugaban da aka ce batun ɗaurin aure ne ke jigon zuwanshi, to me za ka yi zato daga gare shi? Amma muna fata ziyarar ta zamo wani mabuɗin alheri ne ga al’ummar jihar da Jihar baki ɗaya”, in ji ta.
Gwmnatin jahar ta sanar da ranar Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin ba su damar tarbar shugaban ƙasa tare da halartar wajen da zai ƙaddamar da waɗannan ayyuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa.
Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum.
A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu.
Gwamnan ya kara da cewa taimakon da aka bai wa waɗannan ƙungiyoyi zai kara habaka tattalin arzikin al’ummar jihar. Ya yabawa ƙungiyoyin bisa yadda suka tsaya tsayin daka wajen kare muradun membobinsu.
Ya bukaci shugabannin ƙungiyar da su tabbatar da sa ido sosai da kuma ganin cewa an bi dukkan sharuddan shirin. “Hakan zai tabbatar da cewa motocin sun yi aiki daidai da manufa, tare da bai wa shirin damar dorewa da kuma faɗaɗawa don amfanar da wasu a nan gaba’. In ji shi.
Gwamnan ya yaba da rawar da NURTW ke takawa a tattalin arzikin jihar, yana mai bayyana su a matsayin muhimmin ɓangare na samar da kayayyaki, ko a fannin noma, masana’antu ko kasuwanci. Ya ce babu wata harkar rarraba kaya da za ta yi tasiri ba tare da haɗin guiwar NURTW ba.
A cewarsa, gwamnatinsa na saka jari mai yawa a fannin gina hanyoyin mota, inda aka kammala ayyukan hanya guda 26 da aka gada, da kudin da ya kai sama da naira biliyan 100. Haka kuma, an ƙara bayar da kwangiloli don gina tituna 50 masu tsawon fiye da kilomita 850, da kudinsu ya haura naira biliyan 300.
Gwamnan ya bayyana cewa an fara amfani da hanyoyin makamashi masu tsafta, inda aka kusa kammala cibiyar sauya motoci zuwa CNG a jihar. Ya ce wannan cibiya za ta taimaka matuƙa wajen rage farashi da kuma tsaftace muhalli, tare da fa’ida kai tsaye ga ƴan NURTW.
A wani ɓangare na shirin, Gwamna Namadi ya kaddamar da tsarin lamuni na naira miliyan 113 ga ƴan kungiyar mahauta. Shirin zai taimaka wa mutane 53, inda manyan ‘yan kasuwar dabbobi 15 za su samu naira miliyan 5 kowanne, sai sauran 38 da za su samu miliyan 1 kowanne.
Ya ce ana sa ran wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar kiwon dabbobi da samar da nama a jihar, har da kasuwannin nama gaba ɗaya.
Don tabbatar da dorewar wannan ci gaba, gwamnan ya bayyana shirin kafa sabuwar ma’aikatar ci gaban kiwo a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa a matakin farko na shirin, an raba motoci 36 na kasuwanci da darajarsu ta kai naira miliyan 279.3, tare da inshora, ga membobin NURTW karkashin tsarin lamuni na juyi da hukumar Youth Economic Empowerment da Employment ta jihar ke jagoranta.
Usman Muhammad Zaria