Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina
Published: 2nd, May 2025 GMT
A yau Juma’a 2 ga watan Mayu, 2025 Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ke ziyartar Jihar Katsina a karon farko tun bayan hawansa kujerar mulki.
Kamar yadda gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa ta ce, shugaban zai duba wasu muhimman ayyukan da gwamnan ya aiwatar da waɗanda ake cikin yi.
Wakilin mu ya tuntuɓi wasu daga cikin al’ummar jihar domin jin ra’ayoyinsu akan wannan ziyara.
Ya zo ɗaurin auren ’yar gwamna ne — Sabo Musa
Alhaji Sabo Musa shi ne mai bai wa Gwamna Raɗɗa shawara a kan wayar da kan al’umma a harkokin gwamnati, ya bayyanawa wakilinmu cewar, Shugaba Tinubu zai zo Katsina ne domin halartar ɗaurin auren ’yar Gwamna Raɗɗa wanda za a yi a ranar Asabar, 3 ga watan Mayu, 2025.
Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan Legas Gobarar rumbum makamai Maiduguri da Matakan da ya kamata a ɗauka — ƘwararruAkan haka ne aka yi amfani da wannan dama wajen gayyatar shi da ya ƙaddamar da wasu ayyukan da Gwamna Raɗɗa ya aiwatar da waɗanda ake cikin yi.
“Ai ka ga mu a yanzu sai mu ce wani abin alfahari ne ga jama’ar Jihar Katsina domin tun hawan shi mulki ita ce jiha ta farko da ya fara zuwa a Arewa inda ya amsa goron gayyata. Shi ya sa aka yi amfani da damar domin ya ziyarci wuraren da shi Gwamna ya aiwatar da kuma inda ake cikin aiwatar da wasu muhimman aiyuka.”
“A kan haka ma har shi Gwamna ya ba mutanen da ke kusa da masallacin da za a yi wannan ɗaurin aure haƙuri a kan ɗan ƙuncin da za su gani a wannan lokacin. Sannan ya yi kira ga al’umma da su fito domin tarbar shugaban kamar yadda aka san Katsina ɗakin kara ce”, in ji Sabo Musa.
Mun yi zaton ziyarar aiki ce kawai
Mafi yawan mutanen da muka tuntuɓa a kan wannan ziyara sun ce sun yi zaton ziyarar aiki ce.
Malam Halliru ya ce, “farko na yi zaton zai zo duba aikin hanyar da ta tashi daga Katsina zuwa Kano ce da aikin ya tsaya, da kuma batun wutar lantarki mai aiki da iska ta hanyar Rimi wadda ita ma ta yi tsaye cik.
Amma sai kawai na ji an ce, zai zo wajen ɗaurin auren ɗiyar Gwamna ne. Ke nan, babu wani abin a zo a gani da za mu ce na Gwamnatin Tarayya ne wanda ya zo a kan shi”.
Shi kuwa Abu Ƙasim cewa ya yi, ko ba komai a iya cewa jihar ta kafa tarihi daga cikin jihohin Arewa domin a nan zai fara kawo ziyarar yini biyu.
“Ina kyautata zaton cewa, a wannan ɗan lokacin ba zai rasa ganin wasu daga cikin dattawan jihar ba, inda za su bayyana mashi wasu abubuwan da jahar take ciki musamman batun matsalar tsaron da ta addabe mu. Sannan tunda inda zai je wajen duba aikin waccan hanya da aka yi magana wurin da wannan hanyar da aka yi watsi da aikin ta ne, Katsina zuwa Kano, zai ga irin halin da ake ciki da kuma irin ayyukan da shi Gwamna ke yi wanda ko makamantan su ita gwamnatin ta Tarayya ba ta yi su ba.
“Ka ga akwai maganar aikin hanyar jirgin ƙasan da ake cewa wai an dakatar, nan ma ina zaton jama’a za su san irin halin da ake ciki. Na kuma san ƙila zai ɗan yi jawabi a wajen buɗe wancan aiki, ƙila ya faɗi wani abu mai muhimmanci da jahar zata amfana.”
Malama Rabi, wata mai sayar da abinci, ta ce, “ni ina zaton samun abokan ciniki kawai saboda shigowar baƙi, amma in baya ga haka sai in ce banga tasirin wannan ziyara ba. Shugaban da aka ce batun ɗaurin aure ne ke jigon zuwanshi, to me za ka yi zato daga gare shi? Amma muna fata ziyarar ta zamo wani mabuɗin alheri ne ga al’ummar jihar da Jihar baki ɗaya”, in ji ta.
Gwmnatin jahar ta sanar da ranar Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin ba su damar tarbar shugaban ƙasa tare da halartar wajen da zai ƙaddamar da waɗannan ayyuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
A ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da HKI ke yi a kasar labanon a jiya ma ta kai hari a kudancin kasar kuma ta yi sanadiyar mutuwar mauta 4 tare da jikkata wasu guda 3,
Isra’ila ta kai hari da jirgin sama mara matuki kan wata mota a kauyen kafr rumman , kana kuma ta sake kai wani harin a garin kafr sir kamar yadda rahotanni suka bayyana, kuma wadannan hare haren suna zuwa ne kwanaki 3 bayan da sojojin israila suka kai samame ta kasa a kudancin labanon a yankin Nabatiya inda suka kai hari a jiya,
A ranar jumaa da ta gabata ne shugaban kasar ta labanon joseph Aun ya nuna damuwarsa game da ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da Isra’ila ke yi, inda yayi tir da tel aviv game da irin mataken da take dauka na karya yarjejeniyar.
A yan kwanankin nan sakatare janar din kungiyar hizbullah na kasar labanon shaikh Naim Qassem ya jaddada cewa tsayin daka ne karfin labanon, don haka Amurka na matsin lamba ne don ganin an danneta an tauye mata yanci da raunata ta don biyan muradun gwamnati.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci