’Yan bindiga na neman N100m kafin sakin Faston da suka sace a Kaduna
Published: 10th, April 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun nemi a ba su Naira miliyan 100 kafin su sako wani fasto da suka yi garkuwa da shi a Jihar Kaduna.
Faston, mai suna Samson Ndah Ali, mai shekaru 30, yana aiki da cocin Evangelical Church Winning All (ECWA) da ke Mararaba Aboro, a Ƙaramar Hukumar Sanga.
Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi ’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna MutfwangAn sace shi da misalin ƙarfe 1 na daren ranar Litinin, lokacin da ‘yan bindigar suka shiga gidansa.
Faston ya fara aiki a cocin ne ƙasa da makonni biyu kafin wannan lamarin ya faru.
Sakataren cocin, Yusuf Ambi, ya ce yana tare da Faston a daren da lamarin ya faru.
Ya ce washegari an kira shi a waya aka sanar da shi cewa faston ya ɓace.
Da ya isa gidansa, ya tarar ƙofofin a buɗe babu kowa a ciki.
Daga bisani, maharan suka kira, suka nemi a ba su Naira miliyan 100 a matsayin kuɗin fansa.
Ambi ya ce har yanzu suna tattaunawa da maharan.
Dakarun tsaro da suka haɗa da sojoji, ’yan sanda da jami’an DSS sun fara aiki tare don ceto faston.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ce zai yi bayani daga bisani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
Haka kuma ya nemi kotu da ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da kuma 1000.
Baya ga haka, ya buƙaci a umarci su da su nemi gafara ta hanyar wallafa bayani a manyan jaridu biyu na ƙasa.
Amma a zaman kotu na ranar Litinin, wanda ya shigar da ƙarar da lauyansa ba su halarci zaman kotu ba.
Lauyan da ke kare Emefiele da CBN, Mista Chikelue Amasiani, ya sanar da kotu cewa tun da aka shigar da ƙarar, mai ƙarar da lauyansa ba su nuna wata alama ta son ci gaba da shari’ar ba.
Ya roƙi kotun da ta kori ƙarar.
Mai shari’a Ekwo ya amince da buƙatar kuma ya kori ƙarar, inda ya bayyana cewa mai ƙarar zai iya dawo da ita idan ya shirya yin shari’ar da gaske.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp