Wata gobara da ta tashi da sanyin safiyar Lahadi, ta laƙume ƙauyukan Wanori, Sarari, da Nuguri da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno.
Aminiya ta rawaito cewa gobarar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu, da kuma raba daruruwa da muhallin su.
Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza Lakurawa sun kashe ’yan sa-kai 13 a KebbiLamarin dai ya tilasta mazauna ƙauyen Wanori yin ƙaura domin gujewa gobarar da ke ci gaba da yaɗuwa.
Ibtila’in da ya zuwa lokacin wallafa wannan rahoton ba a gano musabbbinsa, ya ƙara dagula wa al’ummar ƙauyen lissafi, kasancewar an samu makamancin hakan a baya, ga kuma ‘yan ta’addan Boko Haram da ke tilasta su yin gudun hijira.
Duk ƙoƙarin da manema labarai suka yi domin jin ta bakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Konduga, Honarabul Abba Ali Abbari, ya ci tura, sai dai wasu mazauna garin sun ce an gano gawarwakin maza biyu, wadanda aka binne tun a ranar Lahadi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Marasa Lafiya A Nasarawa Sun Koka Game Da Yajin Aikin Likitoci
Daga Aliyu Muraki
Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta Kasa reshen Jihar Nasarawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya Lafia ta bi umarnin ƙungiyar ta ƙasa wajen shiga yajin aiki na ɗindindin.
Wakilinmu wanda ya ziyarci asibitin koyarwar, ya bayar da rahoton cewa likitocin sun bar wuraren aikinsu domin matsin lamba ga gwamnatin tarayya ta biya dukkan hakkokinsu da ke karuwa zuwa biliyoyin naira.
A yayin ziyarar, ya ruwaito cewa nas nas da ungozoma ne kawai ke kula da marasa lafiya, musamman a sashen bada kulawar gaggawa, inda suke ƙoƙarin taimaka wa waɗanda ke cikin mawuyacin hali, yayin da ake tura waɗanda lamuransu ke neman kulawar likitoci zuwa wasu asibitoci domin samun kulawar gaggawa.
Haka zalika su ma likitocin Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya (FMC) KKeffisun bi sahun takwarorinsu wajen shiga yajin aikin.
Hakan ya tilastawa marasa lafiya barin asibitocin domin komawa asibitoci masu zaman kansu a cikin biranen biyu, yayin da wasu kuma suka koma gida suna jiran tsammani.
A tattaunawa da wasu marasa lafiya, Gloria Namo da Jamil Ishaq, da ke jinya a asibitocin, sun bayyana damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ta kasa biyan bukatun likitocin, wanda hakan ya hana su ci gaba da samun kulawa.
Sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta biyan dukkan haƙƙin likitocin, ganin cewa ba za su iya zuwa asibitoci masu zaman kansu ba saboda tsadar rayuwa.