Gwamnatin Neja Ta Haramta Karbar Haraji A Hannun Masu Kananan Sana’o’i
Published: 26th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta haramta wa masu tattara kudaden shiga a fadin kananan hukumomi ashirin da biyar na jihar karbar haraji daga hannun ‘yan talla da masu kananan sana’o’i.
Gwamnan jihar Mohammed Umar Bago ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidan gwamnati Minna, babban birnin jihar.
Mohammed Umar Bago wanda ya yi Allah-wadai da yadda ake karbar kudade ba bisa ka’ida ba a hannun kananan ‘yan kasuwa, ya umurci shugabannin kananan hukumomi da kansiloli da su kara sa ido tare da tabbatar da ganin an kawo karshen irin wadannan ayyuka nan take.
Ya tunatar da su cewa gwamnatin jihar Neja tana da tsarin bai daya da ya hana karbar haraji dafa masu kananan sana’o’i domin basu damar dogaro da kai.
“Mun yanke shawarar cewa daga yanzu, babu wwanimai karamar sana’a da za a sake karbar haraji a hannunsa a wannan jihar.”
“’Yan talla da kananan ‘yan kasuwa ba sa biyan haraji a Jihar Neja, kuma duk wanda aka samu yana karbar haraji daga wurinsu zai dandana kudarsa,” inji Gwamnan.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: KASUWANCI karbar haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
Iran ta kaddamar da wasu jerin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila a matsayin maida martani kan haren haren da Isra’ila ta kai wa kasar a cikin daren ranar Juma’a.
Bayanai sun ce hare-haren na Iran sun lalata gine-gine da dama da jikkata mutane yayin da wasu rahotannin ke cewa an samu hasarar rayuka na akalla mutum biyu.
A cewar rahotannin kafofin yada labaran Isra’ila daban-daban, makamai masu linzami na iran sun fada a yankunan Tel Aviv, Haifa, Beersheba da wasu wurare.
An bayar da rahoton barna mafi muni a birnin Tel Aviv, inda akalla makami mai linzami guda ya afkawa wani bene mai hawa 50, lamarin da ya janyo fashewar wani abu mai karfi wanda ya sa hayaki ya tashi a sararin samaniyar birnin.
A cewar darektan cibiyar nazarin dabarun da huldar kasa da kasa, Amir Al-Mousawi, daya daga cikin makami mai linzamin na Iran ya afkawa wata cibiyar binciken nukiliya da ke birnin Tel Aviv.
Wasu rahotanni sun ce an kuma yi nasarar kaiwa ma’aikatar harkokin sojan Isra’ila hari.
Gwamnatin kasar ta sanya takunkumi, inda ta umarci mazauna yankin da kada su buga hotuna ko bidiyo na wuraren da makami mai linzami na Iran ya kai hari, kamar yadda kafar yada labaran Isra’ila ta bayyana.
Birgediya Janar Ahmad Vahidi, da yake magana da gidan talabijin na iran, ya ce martanin na iran mai lakabin Operation True Promise III “zai ci gaba muddin akwai bukatar hakan,” yayin da ya sha alwashin daukar fansar jinin shahidai.
Tun da farko, Vahidi ya ce an kai hari a kalla wurare 150 a harin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.