Majalisar Dokoki Ta Amince Da Kasafin Kudin 2025 Na Kananan Hukumomin Kaduna 23
Published: 25th, February 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kasafin kudi na shekarar dubu biyu da ashirin da biyar na kananan hukumomi ashirin da uku a matsayin doka.
Shugaban Majalisar, Alhaji Yusuf Dahiru Liman, wanda ya jagoranci zaman, ya bayyana cewa an kara kasafin kudin zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku.
Yayin gabatar da kudirin a zauren majalisa don amincewa, Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi da Aiwatarwa, Yunusa Shehu Pambegua, ya bayyana cewa a baya bangaren zartaswa ya mika kasafin kudi na sama da naira biliyan dari da goma sha biyar na kananan hukumomi ashirin da uku na jihar.
Yunusa Shehu Pambegua ya bayyana cewa yayin kare kasafin kudinsu, shugabannin wasu kananan hukumomi sun nemi karin kudi don biyan bukatun ma’aikata da sauran kudaden gudanarwa.
Shugaban kwamitin ya ce bayan da shugabannin kananan hukumomi suka gabatar da yadda suka kashe kasafinsu kuma suka kare sabon kasafin, kwamitin ya gano cewa wasu kananan hukumomi suna bukatar gyara kasafinsu, kuma aka bukaci su rubuta hakan.
Ya ce an sake daidaita kasafin kudin tare da hadin gwiwar hukumomin da abin ya shafa, inda sabon jimillar kasafin kudin ya karu zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku, ciki wanda kashe kudin yau da kullum ya kai kashi sittin cikin dari, yayin da na ayyukan ci gaba ya tsaya a kashi arba’in cikin dari.
Yunusa Shehu Pambegua ya shawarci shugabannin kananan hukumomi da su yi amfani da kasafin kudin yadda ya kamata ta hanyar gudanar da mulki na kowa da kowa don amfanin daukacin al’ummar Jihar Kaduna.
‘Yan majalisar sun amince da kudirin ba tare da sabani ba bayan ya tsallake karatu na uku, kuma yanzu ana jiran amincewar gwamna domin ya zama doka.
Cov/Shamsudeen Manir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Ta Amince Da Kasafin Kudin
এছাড়াও পড়ুন:
Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daba masa wuta.
Bayanai sun nuna cewa barayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.
BBC ya ruwaito mutumin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.
Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), Kwamared Bashir Muhammad, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.