Aminiya:
2025-09-17@23:26:33 GMT

Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn

Published: 5th, February 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci a ƙara adadin kasafin kuɗin shekarar 2025 daga Naira tiriliyan 49.7 zuwa Naira tiriliyan 54.2.

Wannan buƙata na ckkin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wadda aka karanta a zaman majalisar na ranar Laraba.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

A baya, Tinubu ya gabatar wa Majalisar Dokoki kasafin Naira tiriliyan 49.

7 a ranar 18 ga watan Disamba. 2024.

Sai dai a cikin wasiƙarsa, ya bayyana cewa ƙarin da aka yi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga da hukumomin gwamnati suka tara.

Wannna ya haɗa da Naira tiriliyan 1.4 da Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta samu, da Naira tiriliyan 1.2 da Hukumar Kwastam ta samu, da Naira tiriliya. 1.8 da wasu hukumomin gwamnati suka samu.

Bayan karanta wasiƙar, Shugaban Majalisar Dattawa, ya tura buƙatar ga Kwamitin Kasafin Kuɗi don yin nazari cikin gaggawa.

Haka kuma, ya tabbatar da cewa za a kammala duba kasafin kuɗin tare da amincewa da shi kafin ƙarshen watan Fabrairu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Samun Kuɗaɗen Shiga Naira tiriliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.

Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta