Matashiyar da ta watsa wa mai naƙuda tafasasshen ruwa ta shiga hannu
Published: 29th, January 2025 GMT
Wata matashiya mai shekaru 20 ta shiga hannun ‘yan sanda bisa zarginta da ƙona matar ɗan uwanta da ke naƙuda da tafasasshen ruwan zafi.
A tattaunawarta da Aminiya, matashiyar ta ce ɓacin rai ne ya kai ta ga ƙone matar lokacin da musu ya kaure a tsakaninsu.
Jirgin Max Air ɗauke da fasinjoji 59 ya tsallake rijiya da baya a Kano Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?Lamarin ya faru ne a ranar Laraba a garin Dubeli da ke ƙaramar hukumar Yola ta Arewa da ke Jihar Adamawa.
Mijin matar da aka ƙona ya ce yana shago ne inda yake sana’a aka kira shi a waya cewa an watsa wa matarsa ruwan zafi lokacin da take naƙuda.
Kazalika ya nuna takaicinsa na sanin ‘yar uwarsa ce ta aikata ta’asar, kuma jim kaɗan bayan hakan ne matar tasa ta haihu.
A nasa ɓangaren, Kakakin rundunar ‘Yan Sandan Jihar Nguroje ya tabbatar da kama matashiyar da ake zargin, ya kuma ce za su ci gaba da bincike kafin miƙa ta kotu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matashiya Ruwan zafi
এছাড়াও পড়ুন:
Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
A cewarsa, tuni aka shirya wuraren kwana da abinci ga maniyyatan a kasar Saudiyya.
Abdulkadir ya tabbatar da cewa, ana shirye-shirye, inda za a yi alluran rigakafi a ranar 28 ga Afrilu, za a raba tufafi a 30 ga Afrilu, sannan kuma za a raba jakunkuna a ranar 1 ga Mayu.
Ya kara da cewa maniyyatan da suka biya sama da Naira miliyan 8.4 na kudin aikin Hajji, za a biya su bayan sun dawo daga Saudiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp