Aminiya:
2025-06-16@05:27:11 GMT

Matashiyar da ta watsa wa mai naƙuda tafasasshen ruwa ta shiga hannu

Published: 29th, January 2025 GMT

Wata matashiya mai shekaru 20 ta shiga hannun ‘yan sanda bisa zarginta da ƙona matar ɗan uwanta da ke naƙuda da tafasasshen ruwan zafi.

A tattaunawarta da Aminiya, matashiyar ta ce ɓacin rai ne ya kai ta ga ƙone matar lokacin da musu ya kaure a tsakaninsu.

Jirgin Max Air ɗauke da fasinjoji 59 ya tsallake rijiya da baya a Kano Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?

Lamarin ya faru ne a ranar Laraba a garin Dubeli da ke ƙaramar hukumar Yola ta Arewa da ke Jihar Adamawa.

Mijin matar da aka ƙona ya ce yana shago ne inda yake sana’a aka kira shi a waya cewa an watsa wa matarsa ruwan zafi lokacin da take naƙuda.

Kazalika ya nuna takaicinsa na sanin ‘yar uwarsa ce ta aikata ta’asar, kuma jim kaɗan bayan hakan ne matar tasa ta haihu.

A nasa ɓangaren, Kakakin rundunar ‘Yan Sandan Jihar Nguroje ya tabbatar da kama matashiyar da ake zargin, ya kuma ce za su ci gaba da bincike kafin miƙa ta kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matashiya Ruwan zafi

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8

Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

A cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.

Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.

“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.

Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa