Sojojin Najeriya Sun Yi Jana’izar Bangirma Ga Wani Doki A Kaduna
Published: 28th, January 2025 GMT
Runduna daya ta sojojin Najeriya ta gudanar da bikin jana’izar marigayi Mascot, Sajan Dalet Danfari Akawala, a shalkwatar rundunar dake jihar Kaduna. Wanda dokin sojojin ne.
A wata sanarwa da mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya ya fitar, ya ce Kanar Akabike ne ya jagoranci jana’izar, wanda ya wakilci babban hafsan rundunar, Manjo Janar Mayirenso Lander David Saraso.
A cewar sa, Marigayi Sajan Dalet Danfari Akawala ya yi hidimar sashen sadaukarwa da aminci, tare da nuna jajircewa da juriya a gidan Soja.
“Bikin shi ne hanyar mu na girmamawa ta ƙarshe ga wani wanda ya kawo sauyi da farin ciki da aiki tukuru da kuma daukaka sashen da yayi aiki”
Kanar Akabike ya mika ta’aziyyarsa ga daukacin wadanda sukayi aiki da shi da sojojin Najeriya, yana mai nuna jimami game da wannan rashin da aka yi.
Ya kuma yabawa manyan baki da masu jajantawa da suka halarci bikin, yayin da aka yi addu’o’in Allah ya ba shi jajircewa, gwargwado, da kwazon maye gurbin marigayi Sajan Akawala.
A yayin bikin jana’izar, an bayyana Sajan Akawala a matsayin wanda ya fito daga zuriyar Mascot na Sashen, Sajan Farin Doki, wanda ya yi aiki daga 1995 har zuwa rasuwarsa a shekarar 2011. Bayan rasuwar Sgt Farin Doki, rundunar ta samu sabon mascot, Sgt Danfari. Akawala, wanda ya yi aiki har zuwa rasuwarsa a shekarar 2014. Sgt Danfari Akawala’s foal, Sgt Dalet.
An kammala jana’izar ne da addu’o’i da mukaddashin Daraktan (Protestant), Laftanar Kanal Ugwu ya yi, kuma ya samu halartar manyan hafsoshi, sojoji da iyalansu.
PR/Usman Sani/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
Martanin Iran game da ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila na ci gaba a rana ta biyu
Ana ci gaba da mayar da martani mai girma na Iran game da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki.
‘Yan mintoci da suka gabata a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya Na 3”, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta harba daruruwan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan haramtacciyar kasar Isra’ila.
An harba wadannan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki da kuma jiragen sama masu saukar ungulu daga Tehran da sauran garuruwan kasar Iran a matsayin wani mataki na murkushe laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a kan yankunan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya na 3”.
Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun watsa rahoton tashin gobara da hayaki a birnin Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye.
An ga wuta da hayaki na tashi bayan da makamai masu linzami na Iran sun afkawa matatar mai ta Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye. Sannan a cewar bayanan farko, an kashe fiye da mutane 10 a Haifa.