Sojojin Najeriya Sun Yi Jana’izar Bangirma Ga Wani Doki A Kaduna
Published: 28th, January 2025 GMT
Runduna daya ta sojojin Najeriya ta gudanar da bikin jana’izar marigayi Mascot, Sajan Dalet Danfari Akawala, a shalkwatar rundunar dake jihar Kaduna. Wanda dokin sojojin ne.
A wata sanarwa da mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya ya fitar, ya ce Kanar Akabike ne ya jagoranci jana’izar, wanda ya wakilci babban hafsan rundunar, Manjo Janar Mayirenso Lander David Saraso.
A cewar sa, Marigayi Sajan Dalet Danfari Akawala ya yi hidimar sashen sadaukarwa da aminci, tare da nuna jajircewa da juriya a gidan Soja.
“Bikin shi ne hanyar mu na girmamawa ta ƙarshe ga wani wanda ya kawo sauyi da farin ciki da aiki tukuru da kuma daukaka sashen da yayi aiki”
Kanar Akabike ya mika ta’aziyyarsa ga daukacin wadanda sukayi aiki da shi da sojojin Najeriya, yana mai nuna jimami game da wannan rashin da aka yi.
Ya kuma yabawa manyan baki da masu jajantawa da suka halarci bikin, yayin da aka yi addu’o’in Allah ya ba shi jajircewa, gwargwado, da kwazon maye gurbin marigayi Sajan Akawala.
A yayin bikin jana’izar, an bayyana Sajan Akawala a matsayin wanda ya fito daga zuriyar Mascot na Sashen, Sajan Farin Doki, wanda ya yi aiki daga 1995 har zuwa rasuwarsa a shekarar 2011. Bayan rasuwar Sgt Farin Doki, rundunar ta samu sabon mascot, Sgt Danfari. Akawala, wanda ya yi aiki har zuwa rasuwarsa a shekarar 2014. Sgt Danfari Akawala’s foal, Sgt Dalet.
An kammala jana’izar ne da addu’o’i da mukaddashin Daraktan (Protestant), Laftanar Kanal Ugwu ya yi, kuma ya samu halartar manyan hafsoshi, sojoji da iyalansu.
PR/Usman Sani/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos
Wani jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a shataletalen Abbatuwar Phototake da ke birnin Jos a Jihar Filato.
Aminiya ta ruwaito cewa an tabbatar da mutuwar direban da wani fasinja guda ɗaya, tare da jikkatar wasu mata biyu.
Shaidun gani da ido sun ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:00 na safiyar ranar Laraba, bayan tasowar jirgin daga Bukuru zuwa Jos.
Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a GombeWasu mazaunan yankin sun ɗora alhakin faruwar hatsarin kan rashin mutumin da ke kula da shingen tsallaka titin jirgin, wanda ya ratsa titin motoci a daidai shataletalen Abbatuwar Phototake.
Sai dai mai magana da yawun tashar jirgin ƙasa ta Jos, Adam Abdullahi, ya musanta zargin, yana mai cewa direban babur ɗin ne ya ƙi tsayawa duk da gargaɗin jami’in da ke wurin, wanda hakan ya jawo jirgin ya yi ciki da shi.
Bayanai sun ce wannan lamari dai ya fusata mazauna yankin, inda suka shiga jifan jirgin da duwatsu, wanda hakan ya sa jirgin ya gaggauta ƙarawa gaba domin kauce wa tashin hankali.