Aminiya:
2025-06-15@10:12:16 GMT

Matashi ya hallaka mahaifiyarsa da duka a Bauchi

Published: 5th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta cafke wani matashi Safiyanu Dalhatu, mai shekara 20, kan zargin kashe mahaifiyarsa har lahira a unguwar Abujan Kwata.

Kakakin rundunar, Mohammed Ahmed Wakil, ya ce ’yan Kwamitin Tsaro na Unguwar ne suka kai rahoton lamarin ofishin rundunar na ‘A’ Division da ke Bauchi.

Ban taɓa cin zarafin Natasha ba, ina girmama mata — Akpabio Babu abin da zai hana mu zama jam’iyya ɗaya da Kwankwaso — Shekarau

Bincike ya nuna cewar mahaifiyar matashin, Salama Abdullahi, mai shekara 40, ta samu karaya a hannayenta biyu sakamakon dukan da ya mata bayan sun samu saɓani.

Bayan samun rahoto, jami’an rundunar ƙarƙashin jagorancin CSP Abdullahi Muazu, sun garzaya wajen da lamarin ya faru.

Sun kai Salama Asibitin ATBUTH da ke Bauchi, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

Bincike ya nuna cewa matashin ya yi amfani da wani abu wajen dukan mahaifiyar tasa.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike mai zurfi kan lamarin.

Kuma ya ce da zarar bincike ya kammala, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

Bisa rahoton bunkasar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2025, wanda aka gabatar a jiya Juma’a 13 ga wata, an ce a halin yanzu, an samu babban sauyi a tsarin ciniki tsakanin Sin da Afirka, an kuma kyautata tsarin zuwa mai shafar fannoni da dama, mai inganci, mai kunshe da fasahohin zamani, kana a nan gaba za a samu karin damar hadin gwiwarsu a fannonin masana’antu, da aikin noma, da sadarwa, da tattalin arziki ta yanar gizo, da ayyukan more rayuwa, da makamashi mai tsafta, da hada-hadar kudi da sauransu.

A matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma a gun bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka karo na 4, an gabatar da rahoton ne a taron gabatar da shirye-shiryen ayyukan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka, wanda aka gudanar a wannan rana.

Rahoton ya yi bayanin cewa, a shekarun baya-baya nan, an fadada cinikayyar Sin da Afirka, yawan kudin cinikayyar kaya tsakaninsu a shekarar 2023 ya zarce dalar Amurka biliyan 280, kuma yawan kudin cinikin hidimomi a tsakaninsu a shekarar 2021 ya kai sama da dalar Amurka biliyan 41 da miliyan 866, kana an kyautata tsarin cinikinsu.

A daya bangaren kuma, yawan jarin da Sin ta zubawa Afirka ya karu, wanda yawancinsu suka shafi sha’anin gine-gine. Haka zalika, an samu nasarori a fannin gina ayyukan more rayuwa, da gudanar da ayyuka a fannonin sufuri, da wutar lantarki, da sadarwa, da madatsun ruwa da sauransu, da kuma yin hadin gwiwarsu a fannonin ba da ilmi, da aikin noma, da kiwon lafiya, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da sauransu. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa