Angola Zata Shiga Shirin ‘Yankunan Kasuwanci’ Na Kungiyar SADC
Published: 4th, March 2025 GMT
Kasar Angola ta bada sanarwan cewa, zata shiga shirin kungiyar kasashen kudancin Afirka SADC na yankunan kasuwanci, wanda hakan zai bunkasa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen yankin .
Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya bayyana cewa shigar Angola cikin tsarin yankunan kasuwanci, SADC kuma a matsayin mamba na 14 a wannan tsarin zai dauke kudin fito tsakanin kasashen 13 da Angolar.
Labarin ya kara da cewa bayan tattaunawa mai tsawo daga karshe Angola ta sami amincewar mafi yawan kasashen kungiyar ta SADC mai mambobi 16.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba Wa Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
Daga Aminu Dalhatu
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Shugaban Karamar Hukumar Gusau, Alhaji Abubakar Imam, bisa shirin tallafawa jama’a domin dogaro da kai da kuma inganta rayuwarsu.
Ta yi wannan yabo ne yayin bikin kaddamar da kayan tallafi a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta bayyana cewa, kayayyakin da aka raba sun haɗa da motoci, babura, injinan dinki, injinan niƙa, keken guragu, kayan abinci da kuma tallafin kuɗi a fadin ƙaramar hukumar.
Ta bayyana shirin a matsayin abin yabo da ke tallafawa iyalai, wanda ke karfafa dogaro da kai, tare da rage matsin tattalin arziki a tsakanin al’umma.
Uwargidan Gwamnan ta taya waɗanda suka amfana da shirin murna, tare da shawartarsu da su yi amfani da kayan yadda ya kamata domin inganta rayuwarsu da kuma bayar da gudunmawa wajen ci gaban al’umma.
A wani bangare kuma, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta karɓi tawagar mata da suka sauya sheƙa daga jam’iyyun siyasa daban-daban zuwa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai mulki.
Uwargidan Gwamnan ta tabbatar wa sabbin mambobin jam’iyyar da cewa za a ba su dama da haɗin kai a dukkan harkokin jam’iyya, tare da kira gare su da su ba da goyon baya ga hangen nesan gwamnatin wajen tabbatar da zaman lafiya, ci gaban tattalin arziki da dorewar cigaba a fadin jihar.
A nata jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Gusau, Alhaji Abubakar Imam, ya ce an shirya wannan tallafin ne domin taimakawa masu buƙata su dogaro da kansu.