Aminiya:
2025-11-06@07:04:07 GMT

Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa

Published: 4th, February 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu ya ƙi rattaba hannu kan ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi ta Tarayya a Numan da ke Jihar Adamawa.

Hakan na ƙunshe cikin wata wasiƙa da ya aike wa Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas wadda mataimakinsa, Benjamin Kalu ya karanta a yayin zaman majalisar na yau Talata.

Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja

Wasiƙar shugaban ta kare matakin da ya ɗauka na ƙin amincewa bisa la’akari da tanadin da sashe na 22 da ke cikin ƙudirin kafa jami’ar ya yi.

Ya yi bayanin cewa sashen ya yi tanadin cewa filin da za a gina jami’ar zai kasance a ƙarƙashin ikon Gwamnatin Jihar Adamawa wanda ya saɓa wa ƙa’idar kasancewa a ƙarƙashin ikon Gwamnatin Tarayya.

Kazalika, wasiƙar ta Shugaba Tinubu ta kafa hujjar cewa sashe na 25 (b) da ke ƙunshe a cikin ƙudirin bai bayyana cewa jami’ar tana da hurumin da za ta riƙa bayar da shaidar karatun digiri ba.

Idan ba a manta ba, a shekarar da gabata ce Majalisar Wakilan ta amince da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Numan da ke Jihar Adamawa kuma ta miƙa wa shugaban ƙasar domin neman sahalewarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Ilimi ta Tarayya Jihar Adamawa

এছাড়াও পড়ুন:

Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe

Kungiyar Likitoci Mata ta Najeriya (MWAN) reshen Jihar Gombe, tare da hadin gwiwar Hukumar Ci gaba ta Arewa maso Gabas (NEDC), za su gudanar da gwaji kyauta na gano cutar sankarar nono da ta mahaifa ga mata fiye da 500 cikin tsawon kwanaki uku.

Wakiliyar kungiyar MWAN, Dr. Hauwa Saurayi, ce ta bayyana haka a hira da manema labarai a Gombe, a cikin shirin bikin Watan Wayar da Kan Jama’a game da Cutar Sankara.

Ta ce an shirya gwajin ne domin inganta gano cutar tun da wuri da kuma bada magani cikin lokaci, kasancewar cancer na nono da na mahaifa su ne manyan cututtukan sankara da suka fi addabar mata.

Dr. Hauwa Saurayi ta jaddada cewa gano cuta tun da wuri shi ne hanya mafi tasiri wajen rage mace-macen da ke da alaka da cutar sankara, tana jan hankalin mata da su daina jira sai alamun cuta sun bayyana kafin su nemi likita.

A nasa bangaren, Dr. Bawa Gift, Babban Likita (Senior Registrar) a Sashen Tiyata na Asibitin FTH Gombe, ya bayyana sankarar nono a matsayin cutar sankara da ta fi yawaita a tsakanin mata a duniya, tare da gargadi cewa karuwar yawan masu kamuwa da ita na kara zama babbar barazana ga lafiyar al’umma.

Ya ce wani binciken shekara ta 2022 ya tabbatar da cewa gano cutar da wuri da kuma kula da ita cikin lokaci na iya kara tsawon rayuwar marar lafiya, ko da ba a iya warkarwa gaba daya ba.

Dangane da sankarar mahaifa, Dr. Halima Faruk, Farfesa Mai Dangi (Associate Professor) a fannin Gynaecologic Oncology na FTH Gombe, ta bayyana cutar a matsayin “daga cikin cututtukan sankara mafi yawan yiwuwa a kare su amma mafi nauyi ga mata” a duniya.

Ta bayyana cewa kimanin sabbin mutane dubu 500 ke kamuwa da cutar sankarar mahaifa a duk shekara a fadin duniya, fiye da rabinsu na rasa rayuwa, musamman a kasashe masu karamin karfi irin su Najeriya.

Hudu Shehu Ibrahim/Gombe

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri
  • Zulum ya bai wa hukumomin tsaro kyautar motoci 63 don inganta tsaro a Borno
  • Matan 500 Za Su Amfana da Gwajin Cutuka Kyauta a Jihar Gombe
  • HOTUNA: Mun kori jami’ai fiye da 100 cikin shekara guda — DSS
  • Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU
  • Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokar Kafa Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani
  • Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
  • China ta yi martani kan barazanar Trump ta kai hari Najeriya
  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa