Aminiya:
2025-06-16@00:44:53 GMT

Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa

Published: 4th, February 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu ya ƙi rattaba hannu kan ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi ta Tarayya a Numan da ke Jihar Adamawa.

Hakan na ƙunshe cikin wata wasiƙa da ya aike wa Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas wadda mataimakinsa, Benjamin Kalu ya karanta a yayin zaman majalisar na yau Talata.

Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja

Wasiƙar shugaban ta kare matakin da ya ɗauka na ƙin amincewa bisa la’akari da tanadin da sashe na 22 da ke cikin ƙudirin kafa jami’ar ya yi.

Ya yi bayanin cewa sashen ya yi tanadin cewa filin da za a gina jami’ar zai kasance a ƙarƙashin ikon Gwamnatin Jihar Adamawa wanda ya saɓa wa ƙa’idar kasancewa a ƙarƙashin ikon Gwamnatin Tarayya.

Kazalika, wasiƙar ta Shugaba Tinubu ta kafa hujjar cewa sashe na 25 (b) da ke ƙunshe a cikin ƙudirin bai bayyana cewa jami’ar tana da hurumin da za ta riƙa bayar da shaidar karatun digiri ba.

Idan ba a manta ba, a shekarar da gabata ce Majalisar Wakilan ta amince da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Numan da ke Jihar Adamawa kuma ta miƙa wa shugaban ƙasar domin neman sahalewarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Ilimi ta Tarayya Jihar Adamawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran

Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.

“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.

“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.

“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”

Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran