2025-09-20@09:23:52 GMT
إجمالي نتائج البحث: 2669

«Jiragen Ruwa ta»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadi kan mummunan sakamakon Shirin Isra’ila na fadada ayyukanta a birnin Gaza Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya yi gargadi kan mummunan sakamakon matakin da haramtacciyar kasar Isra’ila zata dauka na fadada ayyukan soji a birnin Gaza, yana mai yin Allah wadai da manufofin fadada gine-ginen matsugunan yahudawa ‘yan mamaya a yankunan gabar yammacin kogin Jordan. A jawabin da ya yi wa manema labarai a jiya Alhamis, gabanin taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a hedkwatar Majalisar dake birnin New York, Guterres ya bayyana cewa, matakin farko da gwamnatin mamayar Isra’ila ta dauka na kwace birnin Gaza ya sanar da wani sabon yanayi mai hadari. Ya kara da cewa “fadada...
    A yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya sanar da cewa, ya zuwa yanzu akwai shugabanni da tsoffin ‘yan siyasa da manyan jami’ai, da jakadun dake kasar Sin da sauransu kusan 50 daga kasashe 30 na Turai da suka tabbatar da za su halarci bikin da za a yi albarkacin cika shekaru 80 da samun nasara a yaki da kutsen Japan da yaki da mulkin danniya a duniya. Wannan ya nuna niyyarsu ta hada hannu wajen tunawa da tarihi da kiyaye zaman lafiya da adalci.   Guo ya jaddada cewa, kasar Sin ta shirya bikin ne da nufin tunawa da tarihi da magabata, da kiyaye zaman lafiya da ma tabbatar da makoma mai kyau ga bil...
    Nafisa wacce ta wakilci Nijeriya a karkashin Kwalejin Tulip International ta Nijeriya, ta buge abokan karawarta fiye da 20,000 daga kasashe 69, ciki har da kasashen Turanci.   Gasar ‘TeenEagle’ babbar gasa ce ta duniya wacce ke bibiyar ƙwarewar ɗalibai cikin harshen Turanci, kaifin basira, da ƙwarewa a salon magana. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Sanadiyyar ambaliyar ruwa a gonaki amfanin gona na miliyoyin Naira ne suka salwanta inda ɗaruruwan filayen noma suka shefe da ruwa a Jihar Taraba. Kodayake, ba a bayyana ko an sako ruwa daga Logdo Dam ba ne daga jamhuriyar Kamaru ba, amma kogin Benuwe da ke Taraba ya yi ta malala daga gaɓarsa wanda ya yi sanadin ambaliya da lalata ɗaruruwan filayen noma. ACF ta yi Allah-wadai da rushe kasuwar Alaba Rago Gwamnatin Gombe da Rotary sun yi shirin rage mutuwar mata da yara Daily Trust ta gano cewa ruwan ya fara ƙaruwa a kogi a ’yan kwanakin da suka gabata, kuma a yanzu kogin ya yi ta malala a gefan koguna inda ya haddasa ambaliya a faɗin jihar. Ambaliyar...
    Gwamnatin Jihar Gombe tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Rotary International sun ƙaddamar da shirin aikin jinya domin rage mace-macen mata da yara a faɗin jihar. Shirin da aka gudanar a Ƙananan hukumomi uku da suka haɗa: Gombe da Kaltungo da Yamaltu-Deba, inda aka yi wa jama’a gwaje-gwaje, jinya da wayar da kai a unguwannin Yelenguruza da Kagarawal. An kama Ɗan sanda kan harbe soja a Bauchi Gwamnati ta kara kudin yin fasfo zuwa N100,000 da kuma N200,000 Shugaban Rotary Reproductive, Maternal and Child Health a Nijeriya, Farfesa Emmanuel Adedolapo Lufadeju, ya bayyana cewa fiye da mutum 120 aka duba a unguwar Kagarawal kaɗai, inda aka samu kashi 70 cikin 100 sun kamu da zazzaɓin cizon sauro. Ya ce, tun daga...
    Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa ya bayyana cewa: Shirin dawo da takunkumi kan Iran za shafi mu’amalar Iran da IAEA Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa, Kazim Gharib-Abod yayin da ya dawo daga shawarwarin karshe na shawarwarin da aka yi tsakanin Iran da tawagar kasashen Turai uku a birnin Geneva, ya bayyana cewa: A cikin wannan zagaye na shawarwarin, Iran ta bayyana a fili ga kasashen Turai cewa, ba su da hurumin aiwatar da doka ta yadda za a iya sake dawo da takunkumi da wa’adinsa ya kare kan kasar Iran, kuma babu wata hujja ta shari’a kan matakin...
    Rahoton yahudawan sahayoniyya ya tabbatar da cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ta kasa dakile hare-haren dakarun Yemen Jaridar haramtacciyar kasar Isra’ila ta Jerusalem Post ta bayyana a cikin wani rahoto na baya-bayan nan cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila na fama da babbar matsala ta soji da tsaro, bayan da ta kasa dakatar da hare-haren da Yemen ke kai mata hari da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki tun daga ranar 19 ga Oktoban shekara ta 2023. Jami’an gwamnatin mamayar Isra’ila sun bayyana bangaren Yemen a matsayin “wanda ya fi kowa hauka a yankin,” suna masu gargadin cewa shiga fafatawar da suke yi da su zai haifar da mummunan sakamako ga haramtacciyar kasar Isra’ila, ganin yadda suke ganin dakarun Yemen...
    Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa Birtaniya, Faransa da Jamus suna shirye-shiryen mayar da takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta kakabawa Iran a shekarun baya. Kasashe uku na Turai, da aka fi sani da E3, sun gana da jami’an Iran a ranar Talata a wani abin da aka bayyana a matsayin dama ta karshe na ceto huldar da ke gabansu na yin amfani da batun yarjejeniyar nukiliyar 2015, wanda wa’adinsa zai  kare a tsakiyar watan Oktoba. Duk da cewa jami’an diflomasiyyar Turai sun yi iƙirarin cewa tattaunawar ba ta samar da hanyoyin warware batun kamar yadda suke bukata ba, amma Tehran ta nanata cewa tana nan a shirye don tattaunawa mai ma’ana, muddin aka mutunta haƙƙinta da...
    A lokacin ziyarar, ya gana da Shugaban Brazil, Luiz Inácio Lula da Silva, da sauran manyan jami’an ƙasar. Ƙasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniya guda biyar da suka shafi sufurin jiragen sama, harkokin waje, kimiyya da fasaha, da kuma noma, da wasu muhimman fannoni a ci gaban Nijeriya. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    ’Yan bindigar da suka sace wani mutum, matarsa da ’yarsu a Jihar Katsina, na neman Naira miliyan 600 a matsayin kuɗin fansa. Wanda aka sace sun haɗa da Anas Ahmadu mai shekara 33, matarsa Halimat, da kuma ’yarsu Jidda. Ba zan tsaya takarar kowanne irin mukami ba a 2027 – El-Rufai NAJERIYA A YAU: Matakan da ciwon suga ke bi kafin illata mai fama da shi An sace su ne a gidajensu da ke Filin Canada Quarters a Sabuwar Unguwa, cikin garin Katsina da safiyar ranar Talata. A yayin kai harin, wani ɗan sa-kai mai shekara 25 mai suna Abdullahi Muhammad, ya rasu lokacin da yake ƙoƙarin ceto su. Wani ɗan uwan ma’auratan ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar...
      Lardin Hubei shi ma ya bi sawu, inda ya bullo da nasa shirye-shiryen na raba takardun tallafin tare da mai da hankali musamman a kan bangaren da ya shafi cin abinci. Babban makasudin hakan shi ne a karfafa mutane su rika fita zuwa gidajen cin abinci. Wannan ya kara farfado da salon cin abinci tare a tsakanin Sinawa da kuma kwarya-kwaryan harkokin da ake yi a gefen wasu tituna bisa tsari. Baya ga bunkasa tattalin arziki, wannan dabara tana samar da yanayi mai dadi da faranta ran jama’a.   Shi ma birnin Shanghai ba a bar shi a baya ba a kan wannan sabga, inda shi kuma ya mayar da hankali a kan nishadantarwa ta fuskar al’adu. Birnin ya...
    Shugaban hukumar kula da jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya ce ya ɗauki alhakin hatsarin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da ya auku a ranar Talata. Aminiya ta ruwaito cewa hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11 na safe bayan jirgin ya taso daga Abuja zuwa Kaduna. Dilan ƙwaya ya shiga hannu a Borno ASUU: Malaman Jami’ar FUK sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura  Da yake zantawa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Opeifa ya ce ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen binciken abin da ya haddasa lamarin. “Bayan neman gafarar ’yan Najeriya, a matsayina na shugaban hukumar, na ɗauki alhakin duk abin da ya faru,” in ji shi. “Ba...
    Ƙungiyar Malaman Jami’a (ASUU) reshen Jami’ar Tarayya Kashere (FUK), ta yi zanga-zangar lumana, inda ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aiwatar da yarjejeniyar da suka yi da sauran buƙatunsu da ba a cika ba. Zanga-zangar ta fara ne daga ofishin ƙungiyar, ta bi ta ginin shugaban jami’ar, sannan ta ƙare a bakin ƙofar shiga makarantar. Dilan ƙwaya ya shiga hannu a Borno Ambaliya: Gwamnatin Yobe ta samar wa magidanta 250 matsugunin wucin gadi Shugaban ASUU na jami’ar, Dakta Shehu El-Rasheed, ya ce gwamnati ta kasa cika alƙawuran da suka jawo yajin aikin watanni takwas a shekarar 2022. Ya ce har yanzu ba a biya malamai albashin baya ba, haka kuma babu ƙarin albashi na tsawon shekaru. Ya ja hankalin gwamnati cewa...
    Ƙungiyar Malaman Jami’a (ASUU) reshen Jami’ar Tarayya Kashere (FUK), ta yi zanga-zangar lumana, inda ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aiwatar da yarjejeniyar da suka yi da sauran buƙatunsu da ba a cika ba. Zanga-zangar ta fara ne daga ofishin ƙungiyar, ta bi ta ginin shugaban jami’ar, sannan ta ƙare a bakin ƙofar shiga makarantar. Dilan ƙwaya ya shiga hannu a Borno Ambaliya: Gwamnatin Yobe ta samar wa magidanta 250 matsugunin wucin gadi Shugaban ASUU na jami’ar, Dakta Shehu El-Rasheed, ya ce gwamnati ta kasa cika alƙawuran da suka jawo yajin aikin watanni takwas a shekarar 2022. Ya ce har yanzu ba a biya malamai albashin baya ba, haka kuma babu ƙarin albashi na tsawon shekaru. Ya ja hankalin gwamnati cewa...
    Shugaba Bola Tinubu ya yi alƙawarin hanzarta aiwatar da ci gaban Nijeriya ta hanyar amfani da fasahar kere-kere da tattalin abinci don samun nasarori irin na sauran ƙasashe masu tasowa kamar Brazil. A yayin da yake jawabi a ranar Talata a lokacin da ya gana da wasu ‘yan Nijeriya mazauna kasar Brazil, shugaba Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kawo sauyi ta hanyar kere-kere, gyare-gyare, da kuma samar da ci gaba mai dorewa. Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi  “Dole ne mu sanya Nijeriya a gaba wajen ci gaban Afirka, ta hanyar amfani da fasahar kere-kere, tattalin abinci,...
    Ministan harkokin wajen kasar Venezuela ya bayyana jin dadinsa ga hadin kai da goyon bayan Iran ga kasarsa A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Iran, ministan harkokin wajen kasar Venezuela ya yabawa irin hadin kai da goyon bayan Iran ga ‘yancin kai, yana mai jaddada aniyar Iran na kare ta daga barazanar Amurka. Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya tattauna da takwaransa na kasar Venezuela Ivan Gil Pinto ta wayar tarho game da alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kuma ci gaban da ake samu a yankin Caribbean. A cikin wannan kiran, Ministan Harkokin Wajen Venezuela ya ba da rahoto kan abubuwan da ke faruwa a yankin Caribbean bayan karuwar barazanar Amurka da...
    Rasha ta ba da shawarar tsawaita kudurin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran Mataimakin wakilin dindindin na kasar Rasha a Majalisar Dinkin Duniya Dmitry Polyansky ya sanar da cewa, Rasha ta gabatar da shawarwarin a Majalisar Dinkin Duniya na tsawaita sahihancin kudurin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran. Tashar talabijin ta Russian Today ta ruwaito cewa: Polyansky ya shaida wa manema labarai cewa: “Wannan ba batun sassauta takunkumi ba ne na tsawon watanni shida, amma a maimakon haka, a tsawaita kuduri mai lamba 2231. A gaskiya ma, Rasha da Chana, a matsayin masu kula da shirin hadin gwiwa na shirin (JCPOA), suna son ba da karin sarari ga diflomasiyya da...
    Uzodimma ya ce ƙarin albashi zai inganta rayuwar ma’aikata, sannan ya bunƙasa tattalin arziƙin jihar. Ya kuma bayyana cewa kuɗaɗen shiga na cikin gida sun ƙaru daga Naira miliyan zuwa sama da Naira biliyan uku a kowane wata, yayin da bashin jihar ya ragu daga sama da Naira biliyan 280 a shekarar 2020 zuwa Naira biliyan 100. Ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa cire tallafin mai, yana cewa duk da ya jawo tsadar rayuwa, amma ya ƙara yawan kuɗin da ake raba wa jihohi kuma ya bai wa gwamnati damar yin sauye-sauye. Gwamnan ya ƙara da cewa daga ranar 27 ga watan Agusta, gwamnati za ta fara biyan kashin ƙarshe na kuɗaɗen fansho da ake bai wa tsoffin ma’aikata,...
    Haka kuma, a wani samame daban da rundunar ta kai a ranar 15 ga watan Agusta, 2025, ‘yansanda a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu sun yi artabu da ‘yan bindiga a kusa da garin Dankade. Sun ceto mutum biyu da aka sace; Tukur Bello da Isyaka Abubakar, waɗanda aka sace a dajin Gairi na Jihar Zamfara a ranar 9 ga watan Agusta yayin da suke kiwon shanu. ‘Yansanda sun ce sun ƙwato makamai da harsasai daga hannun ‘yan bindigar, tare da alƙawarin ci gaba da yaƙi da masu garkuwa da mutane a faɗin ƙasar nan. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp...
      Opeifa ya kara da cewa, tuni tawagar kwararru daga Hukumar, jami’an Hukumar Binciken Tsaro ta Nijeriya (NSIB) da sauran hukumomin da abin ya shafa suka isa wurin domin gano musabbabin wannan matsala da kuma tabbatar da daukar matakan kariya. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Hukumar Hisbah ta haramta karuwanci da duk wasu munanan ɗabi’u da ake gudanarwa a otal-otal, wuraren casu da duk wasu cibiyoyin nishaɗi a Jihar Bauchi. Babban Kwamishinan Hisbah, Barista Aminu Balarabe Isah, ya bayyana haka ne a yayin wani taron tattaunawa da masu otal-otal da wuraren shaƙatawa a Bauchi. Trump ya yi barazanar korar Gwamnar Babban Bankin Amurka Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya yi hastari a hanyar Kaduna-Abuja Ya ce an haramta gudanar da al’adun gargajiya irin su Shadi, Sharo, Garaya da kuma shagulgulan wannan zamani kamar Kauyawa Day, Gala, DJ, Aloba da sauransu a bukukuwan aure. Isah ya ce an ɗauki waɗannan matakan ne bayan samun korafe-korafe daga jama’a kan yadda abubuwa na rashin tarbiyya da tayar da...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tarihi ba zai yafe jinkirin yin Allah wadai da bala’in Gaza ba Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bayyana cewa: “Al’umma ta tuna cewa bala’in Gaza bai shafi musulmi kadai ba, wannan lamari ne na gwaji na lamiri na dukkanin bil’adama, don haka suna kira ga dukkanin al’umma ba tare da la’akari da addini ko yanayin kasa ba, da su tsaya a bangaren bil’adama, adalci da mutunci, wato a bangaren dama na tarihi.” Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar a wajen taron baje kolin na majalisar ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, inda ya yi jawabi ga...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tun bayan barkewar yakin da Iran, babu wata hulda da ta hada ta da Amurka Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya jaddada cewa: “Turawa za su iya taka muhimmiyar rawa a shawarwari,” yana mai bayanin cewa: “Tun bayan barkewar yaki da Iran, kasar Iran ta daina yin mu’amala da Amurkawa, amma tana ci gaba da hulda da Turawa ko da a lokacin da ake tsaka da yakin.” A wata hira da jaridar Süddeutsche Zeitung ta Jamus dangane da shawarar da Turai ta gabatar na tsawaita wa’adin aiki da hanyar da za a bi wajen ganin an dawo da takunkumin majalisar dinkin duniya kan Iran, kakakin ma’aikatar harkokin wajen...
    Yau 26 ga watan Agusta take ranar murnar zagayowar bikin Ranar Hausa ta Duniya. A halin yanzu shirye-shirye sun yi nisa domin fara gagarumin bikin Ranar Hausa ta Duniya a birnin Daura, Jihar Katsina. An shirya gudanar da gagarumin bikin na bana a birnin Daura ne, kasancewarsa inda ake gani a matsayin asalin Hausawa, shekaru arau-aru. Mahaya dawaki da sauran mahalarta bikin daga sassa daban-daban na Najeriya da kasashen waje da mazauna garin Daura sun fara tururuwa zuwa filin bikin, wanda zai samu. An kuma shirya gudanar da gagarumin hawan daba a Fadar Sarkin Daura, albarkacin zagayowar bikin Ranar Hausa ta Duniya karo na 10. A wannan ranar ake cika shekara 10 da fara wannan gagarumin biki,...
    Mataimakin Ministan harkokin wajen Iran da takwarorinsa na Faransa, Jamus, da Birtaniyya za su gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawa a birnin Geneva na kasar Switzerland, a daidai lokacin da kasashen uku ke barazanar aiwatar da abin da ake kira tsarin dawo da takunkumin  Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya a kan Iran. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya fada a ranar Litinin cewa, za a koma  yin shawarwari tsakanin wakilan Iran da E3 a ranar Talata. Ya ce za a gudanar da taron ne a matakin mataimakan ministocin harkokin waje da daraktocin siyasa. Hakan na zuwa ne bayan wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da babban wakilin kungiyar EU mai...
    Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Batun cikin gidan kasar Labanon ya jaddada cewa, kungiyar ba za ta taba mika makamanta ba matukar dai Isra’ila na mamaye da wani yanki na Lebanon, ko kuma akwai barazana a kan kasar. A yayin jawabin nasa, Sheikh Naim ya nanata katsalandan din wuce gona da iri da Amurka ke yi a cikin harkokin kasar Labanon, yana mai tabbatar da cewa hukumar kasar ce ke da alhakin kare kasar ta Lebanon, da tsaronta, da kuma ‘yancin kai. Dangane da batun kwance damarar kungiyar kuwa, Sheikh Qassem ya ce matakin gwamnatin Labanon ba shi da tushe balle makama, kuma idan har ta ci gaba da bin wannan tafarki, to kuwa ta mika ‘yancin kan...
    Ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty ya tattauna da takwaransa na Tunisiya Mohamed Ali Nafti kan batutuwa da dama da suka shafi yankin gabas ta tsakiya a gefen taron majalisar ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a birnin Jeddah na kasar Saudiyya. Dangane da ci gaban da halin da ake ciki a Gaza, Abdel Aty ya gabatar da kokarin Masar tare da hadin gwiwar bangarorin shiyya da na kasa da kasa, na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta ba da tabbacin sako mutanen da aka yi garkuwa da su da fursunoni da kuma bude hanyar shigar da kayan agaji. Ya lura da matsaloli na  jin kai da suka biyo bayan manufofin Isra’ila na haifar...
    “Mun yi tattaunawar gaskiya, amma gwamnati tana yi mana wasa,” in ji shi. Ya ce an yi watsi da rahotanni masu muhimmanci, an kafa manufofin da ke cutar da ilimi, sannan an jefa malaman da suka yi ritaya mummunan hali. “Wannan gwamnati ta raina ilimi da malamai. Mun gaji,” in ji shi. Shugaban ASUU ya yi gargaɗin cewa idan gwamnati ta ƙi ɗaukar mataki, za ta ɗauki alhakin duk wata matsala da za ta biyo baya. Ya kuma kira mambobin ASUU da su fito ƙwansu da kwarkwata wajen tarukan da za a gudanar a manyan jami’o’i a ranar Talata, 26 ga Agusta, 2025, yana mai cewa wannan shi ne mataki na farko da ƙungiyar za ta ɗauka don nuna rashin...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pezeskiyan ya godewa kasar Rasha saboda goyon bayanta ga kasar kan hakkinta na tace makamashin uranium, musamman a taron kwamitin tsaron MDD wanda za’a gudanar nan gaba dangane da kudurin kwamatin mai lamba 2231 dangane shirin nukiyar kasar Iran ta JCPOA, Inda kasashen turai 3 wato triko wadanda suke bukatar sake dawoda takunkuman MDD kan kasar ta Iran. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakato Pezeshkiyan yana fadar haka a lokacinda yake magana ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladimir Putun a yau litinin. A nashi bangaren shugaba Putin ya bayyana cewa Rasha za ta tabbatar da cewa sakamakon taron kwamitin tsaro dangane da shirin “snapback” zai fito mai kyau ga kasar Iran....
    Wata mata mai aikin shara da goge-goge, Fa’iza Abdulkadir, ta mayar da kuɗi har N4.8m da aka yi kuskuren tura wa asusun bankinta a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno. Da take zantawa da News Central a Maiduguri, Fa’iza wadda take ɗaukan albashin Naira dubu 30 duk wata ta ce ta yanke shawarar mayar da kuɗin ne saboda tsoron Allah. An yaudari ’yan Nijeriya da suka hana Jonathan lashe Zaɓen 2015 — Ƙungiya Za a yi amfani da Hausa wajen samar da zaman lafiya — Abdulbaqi Jari “Wannan kuɗi ba haƙƙi na ba ne, ba ni na mallaki kuɗin ba, shi ya sa na mayar. Na fi son na zauna cikin kwanciyar hankali da kuma gudun azabar Allah a ranar lahira,”...
    Sojojin Najeriya sun kashe ’yan ta’adda kimanin 35 da ake zargin mayakan kungiyar ISWAP ne a kusa da iyakar Najeriya da Kamaru. ’Yan ta’addan sun taru a yankin Kumshe, wani gari da ke kan iyaka a Jihar Borno, da safiyar Asabar domin kai hari kan sansanin sojoji da ke yankin. Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa bayan samun bayanan sirri, sojojin kasa sun nemi taimakon rundunar sojin sama, inda jiragen yaki suka kai hare-hare a wuraren da aka gano ’yan ta’addan sun taru. “Ranar Asabar, 23 ga Agusta, sojojin runduna ta 21 sun dakile wani hari da ’yan ta’adda suka kai da daddare, inda jiragen yaki suka ragargaza ’yan ta’addan,” in ji wata majiya. Binciken bayan harin ya nuna cewa an...
    Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya jaddada cewa: Hadin kan al’umma, jami’ai, da sojojin da ke dauke da makamai, jan layi ne Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Bayan da makiya suka kasa murkushe al’ummar Iran ta hanyar yaki, a halin yanzu suna neman cimma manufarsu ta hanyar haifar da sabani da rarrabuwar kawuna. Ya ce: “Dukkan jama’a, jami’ai, marubuta, da jaridu, dole ne su kare tare da karfafa garkuwar karfe na hadin kan kasa mai tsarki da dukkan karfinsu.” Jagoran ya jaddada bukatar tallafa wa masu yi wa kasa hidima, musamman ma shugaban kasar wanda ya bayyana a matsayin mai jajircewa da kuzari, yana mai jaddada cewa hadin kan al’umma, gwamnati,...
    Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Gudanar da hidima wa mutane aikin kowa ne Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa yi wa al’umma hidima aiki ne na kowa da kowa, yana mai bayanin cewa hadin kai da fahimtar juna kan kasa suna samun nasarar gudanar da mulki da tsayin daka wajen tunkarar makiya. A yayin jawabin da ya gabatar a wajen bikin sabunta mubaya’ar Imam Khumaini (r.a) a hubbarensa mai tsarki da ke birnin Tehran, shugaban kasar Masar Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: “Aikin hadin kan jama’ar kasa ne yi wa al’umma hidima da nuna musu kauna, idan har za a iya tabbatar da adalci a cikin halayen al’umma, za a yi nasara wajen hidimtawa al’umma, kuma dukkan...
    Kwamandan sojojin Iran ya yi barazanar mayar da martani mai muni da zai haifar da nadama ga makiya Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya jaddada cewa: Sojojin kasar Iran da jarumtarsu suna tsayawa da dukkan karfinsu wajen fuskantar barazanar makiya. A yayin ziyarar da ya kai Jami’ar Kimiyyar Sojin Ruwa ta Imam Khumaini (RA) da ke tashar jiragen ruwa ta Noshahr ta arewacin kasar Iran a jiya Lahadi, Manjo Janar Hatami ya bayyana cewa: “A yau Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da matsayi na musamman a tsakanin kasashen yankin, ya kamata makiya su sani cewa al’ummar kasar na kwarai a cikin sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye suke, kamar yadda suka saba a baya, da...
    Kafofin yada labarai na yahudawan sahayoniyya sun yarda da gazawar dakile Yemen daga ci gaba da ayyukan soji kan Isra’ila Kafofin yada labaran Isra’ila, wadanda tashar 12 da tashar ta 13 ke wakilta, sun amince da cewa: Hare-haren da makiya ke kaiwa kasar Yemen, ya gaza hana sojojin Yemen harba makamai masu linzami zuwa yankunan Isra’ila da aka mamaye. Waɗannan tashoshi na yahudawan sahayoniyya sun yi imani cewa; Da’awar iya dakile hare-haren sojojin Yemen kan yankunan Isra’ila, rudu ne kawai na jami’an haramtacciyar kasar Isra’ila ganin tsawon lokacin da   za a iya dauka domin hana kai waɗannan ayyuka saboda “haɗarinsu.” Tashar talabijin ta yahudawa ta 13 ta yarda cewa harin na baya-bayan nan da aka kai kan kasar Yemen ba...
    Isra’ila ta kaddamar da wani farmaki ta sama a kan babban birnin kasar Yemen Sanaa a jiya Lahadi, inda ta kai hare-hare a yankin kudu maso gabashin birnin San’a. Wakilin tashar Almayadeen ya bayyana cewa, Isra’ila ta kai harin ne kan wani gidan mai  a kudu maso gabashin birnin San’a mallakin kamfanin mai na kasar Yemen da ke kan titin Al-Sitteen, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane  tare da jikkata wasu da dama a lokacin da suke shan mai a motocinsu da sauran ababen hawa a wurin. Kamfanin mai na kasar Yemen ya kuma tabbatar da cewa al’amura sun daidaita an kuma shawo kan gobarar da ta tashi a wurin, tare da kwantar da hankalin ‘yan kasar, kamar yadda wakilin...
    Ɗariƙar Tijjaniyya a Jihar Gombe, ta yi babban rashi bayan rasuwar ɗaya daga cikin fitattun malamanta, Sheikh Umar Bojude. Sheikh Bojude shi ne babban limamin Masallacin Juma’a na Alhaji Gidado Dalibi Yahaya (AG Dalibi). Japan za ta bai wa Najeriya rancen $190m don inganta wutar lantarki Rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC a Gombe Malamin ya rasu a ranar Lahadi, kuma an yi jana’izarsa a unguwar Jan Kai da misalin ƙarfe 5 na yamma. Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ta bakin Daraktan Yaɗa Labaransa, Isma’ila Uba Misilli. Ya bayyana rasuwar malamin a matsayin babban rashi ga ɗariƙar Tijjaniyya, iyalansa da kuma al’ummar jihar. “Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalan marigayi, ɗariƙar Tijjaniyya, Fityanul Islam...
    Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa Najeriya za ta karɓi rancen dala miliyan 190 daga Ƙasar Japan domin inganta wutar lantarki. Wannan na cikin wata sanarwa da ma’aikatar lantarki, yayin da ake gudanar fa taron ƙasashen Afirka da ke gudana a birnin Yokohama na Ƙasar Japan. Mutum 6 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Sakkwato An harbe masu garkuwa da mutane 3 a Kebbi Tawagar Najeriya ƙarƙashin Shugaba Bola Tinubu ta halarci taron. Rancen zai fito ne daga hukumar Japan International Cooperation Agency (JICA), kuma ana sa ran zai taimaka wajen samar da wutar lantarki mai ɗorewa a yankunan da ba su da isasshiyar wuta. Ma’aikatar ta kuma ce wannan lamuni ya zo ne a matsayin ƙari...
    Aƙalla mutane shida sun rasa rayukansu, yayin da har yanzu an nemi wasu uku an rasa, sakamakon kifewar kwale-kwale a Garin Faji na Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Jihar Sakkwato. Lamarin ya faru ne lokacin da mazauna yankin ke tsere wa wani harin ‘yan bindiga da misalin ƙarfe 5:30 na safiyar Alhamis, 21 ga watan Agusta. An tsinci gawar saurayi a gefen kudiddifi a Kalaba Sarkin Musulmi ya ayyana Litinin 1 ga watan Rabi’ul Awwal Wannan shi ne karo na biyu cikin kasa da mako guda da irin wannan ibtila’i ya faru, domin a kwanaki shida da suka gabata, mutane huɗu sun mutu a hatsarin kwale-kwale makamancin wannan a Ƙaramar Hukumar Goronyo ta jihar. Aminiya ta ruwaito cewa, waɗanda...
    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a jihar Kano ta bayyana cewa akwai katin zaɓe na dindindin (PVC) sama da dubu 367,000 da jama’a ba su karɓa ba har yanzu a jihar. Kwamishinan INEC na Kano, Ambasada Abdu Zango, ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi tawagar kwamitin gwamnatin jihar kan rajistar katin zaɓe ƙarƙashin jagorancin kwamishinan yaɗa labarai, Ibrahim Abdullahi Waiya. Ya yabawa matakin kafa kwamitin tare da kira ga mambobinsa da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan jama’a domin su tafi su karɓi katin zaɓensu. Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas 2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba...
    Mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Fluminense Fabio a ranar Talata ya zama mutum na farko a tarihin wasan kwallon kafa na maza da ya buga yawan wasanni a tarihi, lokacin da dan Brazil din ya buga wasa karo na 1,391. Dan wasan mai shekaru 44 a ranar Asabar ya yi daidai da tarihin da tsohon dan wasan Ingila Peter Shilton ya rike na wannan adadin ya samu wannan nasarar a wasan da suka doke America de Cali da ci 2-0 a filin Maracana dake Rio de Janeiro. Kafofin yada labaran Fluminense da na Brazil sun ce a yanzu Fabio ya kasance shi kadai a tarihin kwallon kafa, duk da cewa FIFA ko hukumar CONMEBOL ba ta bayyana hakan...
    Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran, Imam Sayyid Aliyul Khaminae, yace mafarkin da gwamnatin Amurka take yi na JMI ta yi biyayya a gareta, abu ne wanda ba zai taba faruwa ba. Ya kuma yi gargadi ga mutanen kasar su yi hattara da kokarin raba kansu. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Imam Khaminae yana fadar haka a safiyar yau Lahadi a jawabin da ya gabatar a wani taro a cikin Hussainiyyar Imam Khomani (q) dake nan Tehran. Labarin ya kara da cewa Jagoran ya gabatar da jawabin ne, a ranar shahadar Limami na 8 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), wato Imam Aliyu dan Musa Arridah (a). Labarin ya kara...
    Dakarun kare juyin juya halain Musulunci a nan Iran sun nuna goyon bayansu ga gwamnatin JMI, sun kuma yaba da ayyukan da gwamnatinn take yi na kawo ci gaban kasar. Tashar talabijian ta Prestv a nan Tehran ta nakalto dakarun na IRGC na bayyana haka a wani rahoton da suka fitar wanda yayi dai dai da Makon gwamnati a nan Iran. Sun kuma kara da cewa jami’an tsaron kasar suna goyon bayan hadin kan da ke tsakanin bangarorin gwamnati daban daban, da jami’an tsaron kasar. Rahoton yace duk tare da matsalolin da kasar take fama da makiya a waje da cikin kasar amma kasar tana ci gaba, mutane da gwamnati da kuma jami’an tsaron kasar suna aiki tare don ganin...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin kasar Armenia ta yi alkawalin cewa babu wani sojojin Amurka da zai shiga yankin kaukas ta kudu kusa da kanika da kasar Iran. Musamman ta san cewa Iran bata son haka hakama kasar Rasha. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Arachi yana fadar haka, bayan tattaunawa da jami’an gwamnatin Armenia a lokacin da shugaban Iran masoud Pezeshkiyan ya kai ziyarar kasar ta Armenia. Kafin haka dai a makon da ya gabata ne shuga Trump a fadar “White House” ya gana da shuwagabannin kasashen Armenia da Azerbaijan inda suka rattaba hannu a kan yarjeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu, tare da amincewar Armenia ta bawa Azerbaijan damar...
    Jakadann Amurka na musamman a kasar Lebanon Tom Barrack ya bayyana cewa ya yarda da matakan da gwamnatin kasar Lebanon take dauka don kwance damarar kungiyar Hizbulla ta kasar, Shafin yanar gizo na Alarabia na kasar Saudiya ya bayyana cewa Barrack ya shaidawa gwamnatin kasar Lebanon kan cewa yana kirin kungiyar Hizbullah da kuma kasar Iran wadanda dukkaninsu mabiya mazhabar shia ne da sun a cewa su yi aiki da gwamnatin kasar don sasantawa. Kafin haka dai a ranar 7 ga watan Augusta da muke ciki ne gwamnatin kasar Lebanon ta yanke shawarar kwance damarar kungiyar Hizbullah, sannan ta bawa sojojin kasar umurnin wannan aikin. Kuma ta bawa sojojin kan cewa su kammala wannan aikin zuwa watan satumma mai zuwa....
    Gwamnatocin kasashen Iran da Pakisatan sun amince su ninninka yawan kayakin noma na kasuwanci a tsakaninsu. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto minitan noma na kasar Iran Jihad Gholam reza Nouri yaqna fadar haka a jiya litinin ya kuma kara da cewa kasashen biyu zasu karfafa harkokin siyasa da kuma tattalin arziki tsakaninsu, inda suke son ya kai dalar Amurka billiyon $3 daga biliyon $1.4 da yake a halin yanzu. Ya ce suna saran zsu kai wannan adadin a cikin shekaru biyu masu zuwa. Nouri ya bayyana haka ne bayan ya gana da Rana Tanveer Hussain  Na ma’aikatar cibiyar binciken na ayyukan noma na kasar Pakisatan a nan birnin Tehran. Ya ce idan wannan shirin ya kankankama...
    Gwamnatin Tarayya ta rage farashin jinyar ciwon ƙoda daga kimanin N50,000 zuwa N12,000 a Asibitocin Tarayya — ragin da ya kai kashi 76 cikin 100. Wannan saukin farashi ya samu ne bayan amincewar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kamar yadda mai ba shi shawara kan harkokin sadarwa da manufofi, Daniel Bwala, ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin. Bwala ya ce hakan zai kawo saukin rayuwa ga dubban ’yan Najeriya da ke fama da cutar, wadda ke bukatar yin jinya sau da dama a kowane mako. “Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da tallafin tarihi domin rage farashin jinyar ciwon koda ga ’yan Najeriya. An rage farashin kowace wankin ƙoda daga N50,000 zuwa N12,000 kacal,...
    Allah Ya yi wa Alhaji Ahmed Momohsani Ododo, mahaifin Gwamna Ahmed Usman Ododo na Jihar Kogi, rasuwa yana da shekara 83 a duniya. Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa na Jihar Kogi, Kingsley Femi Fanwo, ya sanar da rasuwar a yammacin ranar Litinin, 18 ga Agusta, 2025. Gwamnatin jihar ta bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga iyalan Gwamna da kuma al’ummar jihar baki ɗaya. Sanarwar ta kara da cewa kafin rasuwarsa, Marigayi Alhaji Ododo ya kasance mutum mai daraja wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen gina halaye da dabi’un ɗansa, Gwamna Ahmed Usman Ododo. Ta kuma miƙa ta’aziyya ga Gwamna Ododo, iyalansa da dangin Ododo gaba ɗaya, tare da addu’ar Allah ya ba su ƙarfin juriya da haƙuri.
    Wani mutum ya soka wa budurwarsa mai suna “Ima” wuka har lahira a unguwar Okereke Street da ke garin Fatalkwal na Jihar Ribas. Mutumin, wanda ake wa lakabi da “Doctor” ya daba wa budurwar tasa mai suna “Ima” wuka ne bisa zargin tana cin amanarsa. Lamarin ya faru ne da yammacin Lahadi, wanda shaidu a unguwar suka ce ya samo asali ne daga zargin da Doctor ke yi wa Ima, wanda ya rikide zuwa tashin hankali. Mai kula da gidan da lamarin ya faru ya kai rahoto ofishin’yan sanda na Azikiwe Division, Mile 2 Diobu, wanda hakan ya kai ga cafke wanda ake zargi. ’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa Mutane 62 da aka sace sun tsere...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya barazana ce ga wanzuwar tsaron yankin Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya suna wakiltar wata barazana ga wanzuwa tsaro da zaman lafiyar yankin da kuma kasashensu. Idan ba a dakile wannan barazanar ba, to babu shakka yankin zai fuskanci yake-yake marasa iyaka. A yayin taron manema labarai na mako-mako a ranar Litinin, Baqa’i ya yi ishara da zagayowar ranar 28 ga watan Mordad (19 ga Agusta, shekara ta 1953, yana mai cewa: Ba za a iya mantawa da wannan lamari mai zafi ba, juyin mulkin da ya hambarar da zababbiyar gwamnatin al’ummar Iran tare da hadin gwiwar Amurka da Birtaniya. Dangane da ci...
    Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kebbi da al’ummar jihar bisa rasuwar Sarkin Zuru, Mai Martaba, Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (Gomo II). A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasan shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana rasuwar Sarkin  a matsayin “babban rashi ga ƙasa,” inda ya tuno irin hidimar da marigayin ya yi a matsayinsa na tsohon gwamnan soja na Jihar Bauchi da kuma  hidimarsa a matsayin basarake. Shugaba Tinubu ya lura cewa Najeriya za ta daɗe tana tuna gudummawar tsohon janar ɗin, wanda kuma ya yi yaƙi a matsayin ƙaramin hafsan soja lokacin Yaƙin Basasa. Shugaban ƙasa ya kuma yabawa jagorancin...
    Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu. Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi. Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood A cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekaru 83. Ya ce, rasuwarta babban rashi ne ba ga Shugaban APC kawai ba, har ma da iyalinsa da kuma jam’iyyar APC a Jihar Filato da Najeriya baki ɗaya. Bamaiyi, ya bayyana Mama Lydia a matsayin mace mai tsantseni wajen ibada, jajirtacciyar shugabar mata a...
    Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu. Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi. Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood A cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekaru 83. Ya ce, rasuwarta babban rashi ne ba ga Shugaban APC kawai ba, har ma da iyalinsa da kuma jam’iyyar APC a Jihar Filato da Najeriya baki ɗaya. Bamaiyi, ya bayyana Mama Lydia a matsayin mace mai tsantseni wajen ibada, jajirtacciyar shugabar mata a...
    Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da rabon sabbin baburan hawa ga shugabannin jam’iyyar APC na mazabun kananan hukumomi 12 na shiyyar Jigawa ta Arewa maso yamma wadda Sanata Babangida Hussaini Kazaure ya bayar da kyauta. A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya yaba da kokarin Sanatan tare da shawartar shugabannin da suka sami ababan hawan da su yi amfani da su yadda ya kamata. A jawabin sa, Sanata Babangida Hussaini Kazaure ya ce ya bada baburan ne domin saukakawa shugabannin jam’iyya gudanar da ayyukan su cikin sauki. Ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi bisa nasarorin da ya samu a shekaru biyu da ya yi akan karagar mulki.   Usman Mohammed Zaria
    Gwamnatin Jihar Jigawa tace tana gudanar da ayyukan gyara da ginawa da kuma inganta hanyoyin mota domin cimma kudirin ta na bunkasa bangaren aikin noma. Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka yayin kaddamar da aikin sanya kwalta akan hanyar Dandi da Farin Daba zuwa Gada a karamar hukumar Kazaure. Ya ce gwamnatin jihar ta bada kwangilar aikin ne akan kudi sama da Naira miliyan dubu 8 da miliyan 200 tare da wa’adin kammala aiki a watanni 18. Kazalika, Malam Umar Namadi ya kuma bude aikin gina hanyar Farin Daba, Galo Babba zuwa Galo Karama da aka ba da kwangilar su kan naira miliyan dubu shida da miliyan 300. Ya kara da cewar, aikin zai saukaka wa manoma kai...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Suna sa ido kan abubuwan da ke faruwa a Kudancin Caucasus cikin lura Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, Ismail Baqa’i, ya yi nuni da yadda Iran ke daukan abubuwan da ke faruwa a yankin arewa maso yammacin kasar da muhimmanci, yana mai jaddada cewa: “Suna sanya idanu kan abubuwan da suke faruwa, kuma ba sa sassauci ko daukarsa da rashin muhimmanci.” A wata hira da aka yi da shi ta kafar yada labarai, Baqa’i ya fayyace matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan abubuwan da suke faruwa a yankin Kudancin Caucasus na baya-bayan nan, inda ya jaddada muhimmancin siyasa, tattalin arziki da siyasa a yankin ga Iran da kasashe makwabta musamman...
    Babban sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Ba zasu yarda wasu kasashe su shiga tsakanin Iran da Iraki ba Yayin da yake magana game da rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro tsakanin Iran da Iraki, babban sakataren majalisar koli na tsaron kasar Iran Ali Larijani  ya yi nuni da cewa: Bai kamata a bar kasashe uku su tsoma baki cikin fahimtar juna da tsaron da ke tsakanin kasashen biyu ba, ko kuma su yi amfani da yankin wata kasa a kan wata kasa. Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya tattauna da shirin “Tehran-Tel Aviv” da aka watsa a gidan radiyo da talabijin na kasar Iran kan ziyararsa ta farko a wannan matsayi a kasashen...
    Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo ta ki amincewa da nadin sabon karamin ofishin jakadancin Kenya a birnin Goma Gwamnatin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango ta sanar da kin amincewa da nadin sabon karamin ofishin jakadancin Kenya a birnin Goma da ke gabashin kasar, duba da matakin da ya saba wa ka’idojin diflomasiyya, duba da yadda Kongo ke ganin ci gaba da kasancewa a birnin na Goma ya saba ka’ida. A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar din da ta gabata, mahukuntan kasar Kongo sun bayyana mamakinsu kan sanarwar da fadar shugaban kasar Kenya ta bayar na nadin Judi Kiara Nkumiri a matsayin karamin jakadanta a birnin Goma ba tare da amincewar ma’aikatar harkokin wajen Kongo ba. Sun dauki wannan a matsayin...
    Al’ummar unguwar Jauro Jatau da ke hanyar Bypass a Ƙaramar Hukumar Akko, Jihar Gombe, sun koka kan tsawon watannin da suka shafe ba tare da wutar lantarki ba. Sun roƙi gwamnati, ’yan siyasa da masu hannu da shuni su kawo musu ɗauki cikin gaggawa. Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Zuru Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood Sun bayyana cewa tun watan azumin Ramadan da ya gabata suke cikin duhu saboda rashin tiransufoma, lamarin da ya jefa su cikin ƙunci da wahala. Muhammad Idris Gargajiga, wanda ya yi magana da wakilinmu a madadin mazauna yankin, ya ce duk lokacin da suka kai ƙorafi sai a ce musu yankin ba shi da rumfar zaɓe, abin da suka kira da...
    Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, ta bayyana alhininta game da rasuwar Sarkin Zuru na Jihar Kebbi, Mai Martaba Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya) Gomo II, wanda ya rasu yana da shekaru 81. Shugaban ƙungiyar, Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce marigayin jagora ne mai kishin ƙasa, dattijo nagari kuma basarake mai daraja wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Najeriya hidima. Ta’aziyyar Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025) Adam A. Zango ya auri jarumar Kannywood A cikin sanarwar ta’aziyyar da mai magana da yawunsa, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya tuna irin rawar da Sarkin ya taka a aikin soja. Ya ce Sarkin ya taka rawa sosai lokacin da ya yi Gwamnan soja na tsohuwar Jihar Bauchi,...
    Sarkin Zuru, Alhaji Mohammed Sani Sami Gomo II, ya rasu a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, a wani asibiti da ke birnin London bayan gajeruwar rashin lafiya. Ya rasu yana da shekaru 82. A cewar majiyoyin danginsa, ana sa ran za a kawo gawarsa daga London zuwa Najeriya nan da gobe (Litinin), domin gudanar da jana’iza. Marigayin ya bar mata hudu, ’ya’ya bakwai da jikoki biyu. Daya daga cikin masu rike da sarautar gargajiya a Zuru, Muhammed Abba Zuru, ya bayyana cewa iyalan marigayin na jiran isowar gawarsa daga London kafin a kammala shirye-shiryen jana’iza. An haifi Mohammed Sani Sami a Zuru, Jihar Kebbi, a ranar 24 ga Oktoba, 1943. Ya shiga Rundunar Sojin Najeriya a ranar 10 ga...
    Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya aika da jajensa ga mutane da Firai ministan kasar Pakisatan kan ambaliyar ruwa da ta faru a kasar bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla 300 da kuma bacewar wasu. Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya bayyana cewa shugaban y ace kasar Iran a shirye take ta bada agaji ta kuma aike da yan kwana-kwana don taimakawa kasar fita daga wannan halin da take ciki. Shugaban yayi fatan warkewa da sauri ga wadanda suka jikata ko suka ji ciwo a sanadiyyar wannan ambalin ruwa a kasar ta Pakisatn. Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya jawo ambaliyar ruwa mai yuwa, ya kuma rufe gidaje,...
    Shugaban Iran Masoud Pezeshkian na Shirin wata kai wata muhimmiyar ziyara a kasashen Armeniya da Belarus. A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, mai baiwa shugaban kasar shawara Mahdi Sanaei, ya ce Pezeshkian zai bar Tehran zuwa Yerevan a ranar Litinin din nan, sannan ya wuce Minsk. Ya kara da cewa, a ziyarar ta kwanaki biyu da shugaban zai  kai, yana shirin tattaunawa da manyan hukumomin Armeniya da Belarus, kan hanyoyin da za a bi wajen fadada dangantakarsu, musamman a fannin kasuwanci, da kuma sanya hannu a kan takardun yarjeniyoyi a tsakaninsu. Sanaei ya kara da cewa an shirya kai ziyara a kasashen Armenia da Belarus a karshen watan Yuni, amma aka dage. Ya...
    Firaministar kasarDenmark Mette Frederiksen, wadda a halin yanzu kasarta ke rike da shugabancin kungiyar Tarayyar Turai ta bayyana a wata sanarwa ga manema labarai a jiya Asabar cewa, kasarta na shirin kakabawa Isra’ila takunkumi, sakamakon yakin da take yi a zirin Gaza da yammacin kogin Jordan. A wata hira da ya yi da Jyllands-Posten, Frederiksen ta ce “Yanzu Netanyahu ya zama matsala shi a kan kansa,” tana mai cewa “gwamnatin Isra’ila ta wuce gona da iri.” Ta bayyana halin da ake ciki na jin kai a Gaza a matsayin “mummunan bala’i,” tare da sukar shirin Isra’ila na ci gaba da aikin tsugunar da jama’a a Yammacin Kogin Jordan. Firaministar Denmark ta jaddada cewa kasarta na cikin kasashen da ke neman...
    Jakadan Iran a Saudiyya Alireza Enayati ya tabbatar da ci gaba da tuntubar juna tsakanin babban hafsan hafsoshin sojin Iran da ministan tsaron Saudiyya. A wata hira da kamfanin dillancin labarai na IRNA Alireza Enayati ya yi nuni da cewa, Saudiyya na kallon alakar ta da Iran a matsayin alaka mai matukar muhimamnci, kamar yadda ita ma Iran din take Kallon wannan alaka tsakaninta da Saudiyya.  Inda ya kara da cewa “Mun ga irin goyon bayan da Saudiyya ta bayar kan shawarwarin nukiliyar da aka yi a baya-bayan nan, wanda hakan abin yabawa ne.” Har ila yau, ya yi ishara da cewa, magance da kuma kula da al’amurran da suka shafi yankin gabas ta tsakiya abu ne mai yiyuwa idan...
    Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu a Zirin Gaza ta sanar a yau cewa akalla mutane 70 suka yi shahada da suka hada da 8 da aka gano gawarwakinsu, yayin da wasu 385 suka jikkata a cikin kasa da sa’o’i 24 da suka gabata, sakamakon hare-haren da Isra’ila a sassa daban-daban na yankin. Ma’aikatar ta yi nuni da cewa, adadin wadanda abin ya shafa na ci gaba da karuwa, kasantuwar akwai wadanda suke makale a karkashin baraguzan gine-gine da kuma kan tituna, saboda motocin daukar marasa lafiya da jami’an agaji sun kasa kai musu dauki kawo ya zuwa yanzu. Bisa kididdigar da aka fitar a hukumance, adadin wadanda suka shahada  a yakin ya karu zuwa 61,897, yayin da 155,660 suka jikkata, tun...
    Gwamnatin Jihar Kwara ta ce za ta yi haɗin gwiwa da Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN) da sauran masu ruwa da tsaki domin mayar da jihar cibiyar fitar da kayan gona da na kasuwanci. Kwamishinan Noma da Ci gaban Karkara na jihar, Dakta Afees Abolore, ne ya bayyana haka a wani taron da Hukumar FAAN ta shirya domin sanar da shirin fara jigilar kayayyaki a Filin Jiragen Sama na Ƙasa da Ƙasa na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilori. A cewarsa, wannan shiri na nufin kara inganta matsayin jihar tare da ƙarfafa rawar da take takawa a harkokin kasuwanci na cikin gida da waje. Ya jaddada cewa aikin ya yi daidai da manufofin wannan gwamnati na buɗe sababbin...
    Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa ya mayar da martani ga son zuciya da wani jami’in kasa da kasa ke yi game da mamayar ‘yan sahayoniyya Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya yi tsokaci game da kalaman mataimakiyar shugaban kotun kasa da kasa (ICJ) na goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban mamaki da ya saba wa ka’idojin shari’a da kuma ka’idar rashin son kai na shari’a.” A wata sanarwa dayta fitar a dandalin X, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da harkokin kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya rubuta cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa; Suna godiya ga  Iraki saboda karimcin da ta yi wa masu ziyarar Arba’een na Imam Husain {a.s} Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yaba da kokarin gwamnati da al’ummar Iraki wajen karbar bakwancin masu ziyarar juyayin Arba’een na Imam Husaini {a.s}. A yayin da yake halartar shirin na musamman na “muryar ku a ko’ina” da ake watsawa a gidan rediyon Saba, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya tattauna batutuwan da suka shafi gagarumin tattakin Arbaeen da tasirinsa ga duniyar musulmi. A farkon hirar, minista Araqchi ya mika sakon gaisuwarsa ga masu ziyarar Arba’een a birnin Karbala, inda ya bayyana farin cikinsa da halartar wannan gagarumin taron juyayi. Yana...
    A wasu yankunan Jihar Katsina da suka daɗe cikin fargaba da hare-haren ’yan bindiga, zaman lafiya ya fara dawowa sakamakon sulhu da al’umma suka yi da masu tayar da ƙayar baya. Wannan sulhu, wanda ba a haɗa gwamnati ba, ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin daminar bana. Manoma sun fara noma cikin kwanciyar hankali Ƙananan hukumomin Batsari, Jibiya da Ɗanmusa na daga cikin wuraren da aka samu wannan ci gaba. Wasu manoma da wakilinmu ya zanta da su sun bayyana farin cikinsu da yadda rayuwa ke dawowa dai-dai. Malam Rabe, manomi daga Nasarawa a Ƙaramar Hukumar Jibiya, ya ce: “Mu kam yanzu sai mu ce Alhamdulillahi. Lallai sulhu alheri ne a tsakanin al’umma. Ni rabon da na...
    An kammala taron tattaunawa tsakanin shugaban kasar Rasha Vladimir Putin da takwaransa na Amurka Donald Trump a birnin Alaska na kasar Amurka, inda bangarorin biyu suka bayyana taron a matsayin mai matukar amfani. Fadar Kremlin ta tabbatar da cewa tattaunawar ta yi armashi, yayin da manzon musamman na Rasha Kirill Dmitriev ya bayyana cewa yanayin taron ya yi kyau. Putin ya jaddada aniyar kasashen biyu na kawo karshen kiyayyar da suke yi da kuma bukatar cimma matsaya domin kawo karshen yakin Ukraine. Ya yaba da yadda Trump ya fahimci muradun Rasha da kuma burinsa na fahimtar ainihin rikicin. A nasa bangaren, Trump ya tabbatar da cewa tattaunawar ta kai ga cimma matsaya a kan batutuwa da dama, yayin da wasu...
    “Tsarin mulkin ADC ta bayyana cewa duk wanda ke neman zama shugaban jam’iyyar, dole ne ya kasance mamba nagari na jam’iyya. Wannan shi ne muhimman bukata ta asali wadda ba za a iya yin watsi da ita ko kauce mata ta kowace hanya ba. “A cewar tsarin mulkin ADC, hanyar da ta dace don cike gurbin jagoranci bayan tafiyar Cif Nwosu ita ce, ta hanyar taron kwamitin zartarwa na kasa.” Tsaagin jam’iyyar ta sake tabbatar da cewa Alhaji Nafiu shi ne halastaccen shugabanta na kasa tare da kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da hadin kai. Ya kuma bayyana kwarin giwa kan ikon hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na kiyaye...
    Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka yi a garin Potiskum a daren Juma’a zuwa safiyar yau Juma’a ya haifar da ambaliya, wanda ya haifar da tashin hankali ga mazauna garin.   Kamar yadda majiyar da ke garin ta shaidawa Aminiya cewa, ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka fara shi tun kusan tsakar daren Alhamis ya yi sanadiyyar rugujewar gidaje da dama, inda wasu gine-gine suka ruguje ƙarƙashin ruwan. An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil Sakamakon ambaliyar ruwan ya sa mazauna wasu unguwanni da dama suka rasa matsugunansu inda suke hijira ya zuwa gidajen ‘yan uwa da makarantu, inda suke kokawa kan yadda iftala’in ta afku....
    “Sama da yara miliyan 10.1 ne ba su kai makaranta, kashi 70 masu zuwa makarantar kuma ba su da dabarun koyo, kuma fiye da kashi 60 na malaman firamare na gwamnati ba su da ilimin dijital,” in ji ta Da take yaba wa gwamnatin Koriya ta Arewa bisa tallafin da ta samu ta hannun hukumar raya kasashe ta KOICA, Garba ta ce wannan hadin gwiwa ya taimaka wa kasar wajen sake tunanin koyo, tare da dakile rarrabuwar kawuna, da bai wa makarantu da malamai kwarin gwiwa domin samar da sauyi mai dorewa. Mataimakin Babban Sakatare na UBEC (Technical), Mista Razak Akinyemi Olajuwon, ya bayyana cewa, wannan shiri ya kara wa malamai kwarin gwiwar yin amfani da su da bunkasa abubuwan...
    “Manufar ita ce a ninka adadin likitoci, ma’aikatan jinya, masu hada magunguna, kwararrun dakunan gwaje-gwaje da sauran kwararru a fannin kiwon lafiya. Wannan ko shakka babu zai kara habaka harkokin kiwon lafiya a kasar,” in ji shi. Tsohon gwamnan Jihar Katsinan ya bayyana cewa, a bana, TETFund ta samu tallafinta mafi girma na Naira Tiriliyan 1.6, wanda ya haura daga kaso 3 na harajin ilimi da aka dora wa ribar kamfanonin da ke kasuwanci a Nijeriya kamar yadda dokar TETFund ta tanada. Masari ya bayyana cewa, daga cikin Naira Tiriliyan 1.65, an fitar da Naira biliyan 225 zuwa asusun bayar da lamuni na ilimi na Nijeriya (NELFUND), domin shirin rancen daliban gwamnatin tarayya. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna...
    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya bar Abuja domin ziyarar aiki zuwa ƙasashen Japan da Brazil. Ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da misalin ƙarfe 11:15 na safiyar Juma’a, inda zai tsaya a Birnin Dubai na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC Manyan jami’an gwamnati da suka raka shi, sun haɗa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkar Tsaro, Nuhu Ribadu. Sauran sun haɗa da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila; da Ministan Kuɗi, Wale Edun. A Japan, Shugaba Tinubu zai halarci Taron Ci Gaban Afirka karo na tara (TICAD9)...
    Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ta bayyana cewa ƙimar hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya ta sauka zuwa kashi 21.88% a watan Yuli 2025, daga kashi 22.22% da aka samu a watan Yuni 2025. Wannan na nuni da raguwa da kashi 0.34% idan aka kwatanta da watan da ya gabata. Rahoton ya nuna cewa hauhawar farashin abinci na shekara-shekara a watan Yuli 2025 ya kai kashi 22.74%, wanda ya ragu da maki 16.79% idan aka kwatanta da kashi 39.53% da aka samu a Yulin 2024. NBS ta danganta wannan raguwa mai yawa da sauyin shekarar wajen lissafi. Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan...
    A farkon wannan shekarar da ta gabata, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, a wani taro ya bai wa kungiyoyin na Sufurin Jiragen Sama tabbacin cewa, Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da bi ka’ida wajen sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman kasa. Keyamo ya kuma bai wa shugabannin kungiyoyin tabacin cewa, suma a sanya kan batun na yarjejeniyar ta sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman. Kazalika, ba su tabbacin cewa, zai umarci hadiminsa domin ya ci gaba da sanar da shugabannin kungiyoyin kan abinda ke tafiya game da yarjejeniyar. Sai dai, a jawabin da shuwagabbin kungiyar da kuma na ma’aikatan suka gabatar a wani babban taronsu a shalakwar Tashar Jiragen Sama da ke...
    Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani da karfi kan duk wani wuce gona da iri kanta Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani ya bayyana cewa: Gwagwarmaya ita ce babban jari kuma wata dabara mai kima ga yankin, yana mai jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da aka kai mata, kuma babu wata tattaunawa da za ta yi tasiri a karkashin tunanin Amurka na “zaman lafiya da nuna karfi.” Ali Larijani ya jaddada a shirye Iran take a koda yaushe ta mayar da martani mai karfi kan duk wani hari da gwamnatin mamayar Isra’ila za ta kai kan...
    Wata kotun tarayya a kasar Kanada ta ayyana manyan jam’iyyun Najeriya na APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci yayin da ta hana wani tsohon dan siyasa, Douglas Egharevba, mafaka a kasar saboda alakarsa da jam’iyyun. Jaridar Peoples Gazette ta rawaito cewa alkalin kotun, Phuong Ngo, a hukuncin da ta yanke ranar 17 ga watan Yunin 2025, ta hana dan siyasar izinin shiga kasar bayan samun shi da gaza cika sharudan dokar shige da fice ta kasar. A cewar alkalin, “Dabi’ar wasu ’yan siyasa ’yan PDP, wadanda wasu daga cikinsu ma kusoshi ne a jam’iyyar, da wadanda suka aikata laifukan siyasa ko aka yi da yawunsu, ta yi yawan da ba zai yiwu a ki alakanta shugabancin jam’iyyun da ita...
    Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da miƙa wa mataimakinsa, Malam Faruk Jobe, ragamar mulkin jihar, inda shi kuma zai tafi hutun mako uku domin duba lafiyarsa. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labaran jihar, Bala Salisu Zango, ya fitar a ranar Alhamis. Sanarwar ta bayyana cewa hutun zai fara ne daga ranar Litinin, 18 ga watan Agusta, 2025. An zabi sabuwar firaminista a Luthuania Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC A cewar Gwamna Radda, hutun zai ba shi damar samun kulawar likitoci da kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa cikin koshin lafiya. “Cikin matakan da nake ɗauka don kula da lafiyata da kuma ganin na yi...
    A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.   “Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”  ...
    A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.   “Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”  ...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    “Kowa ya sani wadatar abinci yana ɗaya daga cikin alamun da ke nuna kyautatawar tattalin arziki na ƙasa baki ɗaya, don haka ne muka himmatu wajen ba da namu gudunmawar ta wannan fannin.”   Ya kara da cewa, an kafa gidauniyar ne domin taimakawa a ɓangaren kiwon lafiya, ilimi, tattalin arziki wanda rabon takin na daga cikin shirin gidauniyar na bunƙasa tattalin arziki, da kuma kyautata ci gaban al’umma.   “Wannan shi ne karo na huɗu da wannan gidauniyar ta ke rabon taki duk shekara ga manoma masu ƙaramin ƙarfi da ba za su iya sayen takin a irin wannan lokacin da gona ke buƙata ba.”   “An ware buhun taki guda 6,000 da za a rabar wa manoma masu...
    A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.   “Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, sai an biya kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, sai ka bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”   Dan majalisar ya kuma yi...
    “Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya. “Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi. Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara. Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin. “Wannan ziyara tana da...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi tsokaci kan furucin Netanyahu game da kafa ‘Babban Kasar Isra’ila’ Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana a safiyar yau alhamis cewa: Kafafen yada labaran yammacin duniya a al’ada na zargin duk wanda ya ambaci ra’ayin ‘yan sahayoniyya na kafa “Babban kasar Isra’ila” da kiyayya ga wata al’umma. Bayanin Araqchi, wanda aka yi da sanyin safiyar Alhamis a shafinsa na yanar gizo na dandalin sada zumunta na X, yana mai mayar da martani ga kalaman fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu game da batun kafa “Babban kasar Isra’ila.” A cikin shafinsa na yanar gizo, Araqchi ya yi tambaya cewa: “Shin suna daukan furucin Netanyahu kansa a matsayin mai adawa da wata...
    Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya Bayyana cewa: Shugabannin gwamnatin nuna wariyar al’umma suna kokarin yaudarar al’ummar Iran A martaninsa ga fira ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya da ya yi a baya-bayan nan, shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Kasar Iran a yayin da yake gabatar da wasu takardu kan matsalar karancin ruwa da kuma matsalar fari a yankunan da aka mamaye na Falasdinu, ya bayyana cewa; ‘Yan Nazi na karni na 21, wadanda suka kai hari kan babbar tashar ruwa da ke arewacin birnin Tehran a dandalin Tajrish da makami mai linzami, a yanzu haka suna kokarin yaudarar al’ummar Iran da kofin ruwa da aka yi masa magani. Amma al’ummar Iran a tsawon tarihi, sun dauki ko da mafi gogaggen...
    Babban sakataren kungiya Hizbullahi ta kasar Lebanon ya karbi bakwancin Ali Larijani ya kuma godewa Iran bisa goyon bayan da take baiwa kasar Lebanon da ‘yan gwagwarmaya Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Qassem ya gana da Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran da tawagarsa a gaban jakadan Iran a Lebanon Mojtaba Amani. A yayin taron, Sheik Qassem ya jaddada godiyarsa ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran bisa ci gaba da goyon bayan da take baiwa kasar Lebanon da kuma ‘yan gwagwarmaya da yakin da suke yi da makiya yahudawan sahayoniyyar Isra’ila da kuma goyon bayan da take baiwa hadin kai da ‘yancin kai na Lebanon da kuma ci gaba...
    Ƙasar Amurka ta amince ta sayar wa Najeriya makaman da kuɗinsu ya kai Dala miliyan 346, kwatankwacin Naira biliyan 530 don yaƙi da ta’addanci. Makaman da za a siyar sun haɗa da bama-bamai da na’urorin kakkabo jiragen sama da jirage marasa matuka da sauran su. NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai A cewar Kamfanin Sarrafa Makamai na Amurka (DSCA), za a sayar wa Najeriya makaman ne domin tallafa wa shirinta na yaki da ’yan ta’adda da masu safarar miyagun ƙwayoyi. Kamfanin ya sanar da cinikin ne a cikin wata sanarwa ranar Laraba. A cewar sanarwar, Najeriya ta buƙaci sayen bama-bamai guda 1,002, na’urar kakkabo jirage guda 1,002,...
    Lauyan Maïga, Cheick Oumar Konaré, ya bayyana cewa kamun bai dace ba saboda Maïga ba shi da niyyar guduwa ko lalata shaidu, yana kuma zargin cewa wannan wani mataki ne na siyasa saboda tsohon Firaministan ya daɗe yana sukar gwamnatin soja tun bayan tsawaita mulkinsu ba tare da gudanar da zaɓe ba. Maïga, ya hau kujerar Firaminista a watan Yulin 2021 bayan gwamnatin sojoji ta yi juyin mulki, inda ya goyi bayan dakatar da shirye-shiryen zaɓe don bai wa gwamnatin soja ƙarin lokaci. Sai dai daga baya ya fara sukar wasu matakan gwamnati, musamman bayan an dakatar da shi daga kujerarsa a watan Nuwamban 2024. Tun bayan juyin mulkin 2020 da na 2021, Mali ta kasance ƙarƙashin mulkin soja, kuma...
    Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Berri ya tarbi Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran a hedikwatar shugaban kasa ta biyu dake Ain al-Tineh. Larijani ya tabbatar da cewa bayan ganawar da aka yi tsakanin kasashen Labanon da Iran lamarin ya yi kyau da armashi. Ya jaddada cewa Iran ba ta da niyyar yin katsalandan a cikin harkokin cikin gidan kasar Labanon, yana mai cewa bai kamata wasu kasashe su ba da umarni ga gwamnatin Lebanonba, musamman kan wasu batutuwa masu sarkakiya wadanda al’ummar Lebanon ne tare da gwamnatinsu kawai za su iya yanke shawarar a kansu. Larijani ya jaddada cewa Iran ba ta zo da wani shiri a Labanon ba, sai dai Amurkawa sun zo ne...
    Masar ta yi Allawadai da kalaman Benjamin Netanyahu game da abin da ya kira shirinsa na kafa babbar kasar yahudawa ko kuma Isra’ila Babba. Wannan dai ya zo ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Masar ta fitar, bayan da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi magana kan wanann batu, wanda ya tayar da hankulan Larabawa kuma suka yi watsi da shi. Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta ce “tana tabbatar da aniyarta ta abbatar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya tare da yin Allah wadai da abin da wasu kafafen yada labaran Isra’ila suka ruwaito dangane da abin da ake kira Isra’ila Babba. Ya yi bayanin cewa, “ya bukaci a yi karin haske kan hakan, bisa...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Duk da kara wayar da kan direbobi da fasinjoji da Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta ce tana yi, ana kara samun ƙaruwar wadanda ke rasa rayukansu sakamakon hadura a titunan kasar nan. A shafinta na internet, FRSC ta ce a watanni uku na farkon 2024, mutane 1,471 ne suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin mota. Kazalika, a watanni uku na farko na wannan shekara ta 2025, adadin ya haura zuwa mutane 1,593 — karin mutum 122, ko kuma kashi 8.3 cikin dari. NAJERIYA A YAU: Yadda matasa ke bayar da gudunmawa ga ci-gaban al’umma DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci...
    Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan Alhamis din zai bar Abuja domin fita ziyarar aiki a ƙasashen Japan da Brazil, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ta tabbatar. Sai dai gabanin isa ƙasashen biyu, Tinubu zai soma yada zango a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa sannan daga bisani ya ƙarasa Japan. An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe A yayin da shugaban yake Japan, zai halarci taron Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) karo na tara  a birnin Yokohama daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta. Taken taron na bana shi ne “Haɗa Hannu da Afirka Wajen...
    Wasu daga cikin zarge-zargen da ake yi wa shugaban sun hada da kara farashin kudin takin gwamnati daga ₦20,000 zuwa ₦22,000 kan kowane buhu; hada rikici tsakanin shugabannin Siyasar yankin; raba kan Kansilolin karamar hukumar; tsunduma cikin harkokin siyasa masu raba kan jama’a ta hanyar bayar da dukiyar gwamnati ga abokan siyasarsa kawai; da dai sauransu.   Kwamitin majalisar, ya zauna da bangarorin biyu a ranar Talata, 12 ga watan Agusta inda shugaban ya yi watsi da wasu zarge-zargen da cewa, ba su da tushe balle makama, amma ya amince da karin farashin kudin takin gwamnati. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga...
    Ƙungiyar Ci Gaban Masarautar Jama’a (JEDA), ta roƙi Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, da ya kammala manyan titunan Birnin Kafanchan, wanda aikin ya tsaya tun zamanin Nasir El-Rufai. Muƙaddashin shugaban ƙungiyar, Ahmad Usman Husain, ya ce waɗannan tituna na da muhimmanci wajen bunƙasa tattalin arziki da rayuwar yau da kullum a Kudancin Kaduna. Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura Ya ƙara da cewa abin takaici ne a ce ba a haɗa titunan Kafanchan cikin jerin sabbin ayyukan da gwamnan ya ƙaddamar ba, duk da cewa ya yi alƙawarin kammala su a lokacin yaƙin neman zaɓe. Ƙungiyar ta bayyana Kafanchan a matsayin cibiyar...
    Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta dakatar da Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano, Muhammad Nazir Yau, na tsawon wata uku domin gudanar da bincike kan zargin yin amfani da kujerarsa ba bisa ƙa’ida ba. Kansilolinsa sun zarge shi da karkatar da kayayyaki da kuma almundahana wajen tafiyar da dukiyar jama’a. Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno Lafiyar Tinubu kalau – Soludo An yanke wannan hukunci ne bayan majalisar ta karɓi rahoto daga kwamitin karɓar koke-koke na jama’a, wanda shugaban marasa rinjaye na majalisar, Hussaini Lawan Cediyar Yangurasa, ya jagoranta a zaman ranar Laraba. Majalisar ta kuma umarci ma’aikatar ƙananan hukumomi da harkokin masarautu ta jihar da ta bai wa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar damar riƙon...