Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana
Published: 3rd, May 2025 GMT
Babban darektan hukumar kula da tattara bayanai da yada su ta bangaren teku ta kasar Sin, Shi Suixiang, ya bayyana cewa, manufofin tallafi da aka bullo da su a matakai na tsakiya da na kananan hukumomi sun karfafa ci gaban yawon shakatawar.
Ya kara da cewa, gwamnatin tsakiya ta inganta fadada hanyoyin jiragen ruwa da kayayyakin yawon shakatawa yayin da kuma ake kara daidaita tsarin rajistar jiragen ruwa da kuma shigar da su cikin hada-hada.
Wasu manazarta dai sun bayyana cewa, a sa’ilin da lokacin goshin damina ke gabatowa, ana sa ran yawon shakatawa na bakin teku da tsibirai a yankin kudu maso gabashin kasar Sin ya bunkasa, tare da kara samun balaguro ta ruwa da nufin cin gajiyar kasuwannin gabashin Asiya da kudu maso gabashin Asiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
Yau Litinin, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.
Game da halin da ake ciki yanzu a yankin Gabas ta Tsakiya, Guo Jiakun ya ce, ministan wajen Sin Wang Yi ya riga ya tattauna ta waya tare da takwarorinsa na Iran da Isra’ila, inda ya yi kira ga bangarorin biyu su warware rikicin ta hanyar tattaunawa. Ya ce ya kamata bangarorin biyu su dauki matakai nan da nan don hana ruruwar wutar rikicin. Kana Sin za ta ci gaba da yin mu’ammala da bangarorin da abin ya shafa, ta yadda za ta ba da gudunmawa wajen yayyafa ruwa ga rikicin.
Game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu da za a gudanar ba da jimawa ba, Guo Jiakun ya ce, shugabannin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya za su tsara hadin gwiwa a nan gaba tare, da inganta gina al’umma mai makoma ta bai-daya ta kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya mai inganci.
Game da batun zamowar kasar Vietnam kawar kungiyar BRICS, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na maraba da Vietnam ta zama kawar BRICS, kuma ana ganin cewa, Vietnam za ta ba da gudummawa mai kyau ga tsarin BRICS.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp