Babban darektan hukumar kula da tattara bayanai da yada su ta bangaren teku ta kasar Sin, Shi Suixiang, ya bayyana cewa, manufofin tallafi da aka bullo da su a matakai na tsakiya da na kananan hukumomi sun karfafa ci gaban yawon shakatawar.

 

Ya kara da cewa, gwamnatin tsakiya ta inganta fadada hanyoyin jiragen ruwa da kayayyakin yawon shakatawa yayin da kuma ake kara daidaita tsarin rajistar jiragen ruwa da kuma shigar da su cikin hada-hada.

 

Wasu manazarta dai sun bayyana cewa, a sa’ilin da lokacin goshin damina ke gabatowa, ana sa ran yawon shakatawa na bakin teku da tsibirai a yankin kudu maso gabashin kasar Sin ya bunkasa, tare da kara samun balaguro ta ruwa da nufin cin gajiyar kasuwannin gabashin Asiya da kudu maso gabashin Asiya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Za Ta Ci Gaba Da Bullowa Da Dubarun Bunkasar Ta

Gwamnatin jihar Kwara ta sake jaddada kudirinta na kara bude kofa ga al’umma domin ci gaba da kuma sanya jihar ta yadda za ta yi tasiri a duniya ta hanyar sanya hannun jari mai inganci.

 

Kwamishinan Ayyuka na Jiha Injiniya. Abdulquawiy Olododo, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da ayukkan ma’aikatar a taron manema labarai na wata 3 na farkon shekara ta 2025, wanda aka gudanar a dakin taro na ma’aikatar kudi, Ilorin.

 

A cewarsa jimillar ayyuka 46 da ake ci gaba da gudanarwa a cikin kwata na farko na shekarar 2025, daga cikin su 33 an kammala su baki daya, inda a yanzu haka ayyuka 11 ke ci gaba da gudana.

 

Ya kara da cewa, an bayar da sabbin ayyukan tituna guda 24 a shekarar 2025 kadai, inda 6 tuni aka kammala su.

 

Kwamishinan ya bayyana yadda ake ci gaba da gudanar da aikin titin Agbamu – Ila-Orangun, hanya ce mai matukar muhimmanci a tsakanin jahohin kasar da nufin bunkasa harkokin tattalin arziki da kuma inganta hanyoyin shiga tsakanin jihohin Kwara da Osun.

 

Kwamishinan ya kuma sanar da cewa, hukumar kashe gobara ta jihar, ta tanadi kadarorin da darajarsu ta kai ₦728,478,052,012, wanda hakan ke nuni da karfafa tsarin bayar da agajin gaggawa na gwamnati.

 

Ya ci gaba da cewa, aikin titin RAAMP mai tsawon kilomita 209.77 da ake yi ya samu lambar yabo ta kasa guda biyu – Best in Counterpart Funding and Best in General Disbursement – wanda ya nuna kwazon gwamnati.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
  • Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana
  • Sabon Tsarin Ci Gaba Na Sin Ya Kawo Sauyi Daga Samar Da Takalma Miliyan 100 Zuwa Kera Mattarar Bayanai Ta Microchip
  • Masifar Gobara Tana Kara Bunkasa A Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tare Da Fara Raba Yahudawa Da Muhallinsu
  • Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan
  • Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji
  • ’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa na Bayelsa
  • Gwamnatin Jihar Za Ta Ci Gaba Da Bullowa Da Dubarun Bunkasar Ta
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030