A kokarin ta na ci gaba da zaburar da ma’aikatan ta, Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce za ta shirya taron bitar sanin makamar aiki ga jami’an ta dake dawainiya da alhazai a gida da kuma kasa mai tsarki.

Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed umar labbo ya bayyana haka bayan kamala taro na musamman da shugabannin sassa na hukumar da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse babban birnin jihar.

Yayi bayanin cewar, hukumar zata bada bitar ne ga jami’an da kuma shugabannin shiyya-shiyya kan hanyoyin kara kula da walwala da jin dadin maniyyata da kuma dabarun magance kalubale yayin gabatar da aikin hajji.

Yana mai cewar bada horo na da matukar mahimmaci duba da yadda aka fara biyan kudin kujerun aikin hajjin 2026.

Alhaji Ahmed Umar Labbo, yace tuni shirye-shirye sunyi nisa waje fara shirin dunkarar aikin hajjin shekarar 2026.

A cewar sa, tsarin gudanar da aikin hajjin wannan shekarar yasha bam-bam da na shekarar 2024.

Yayi nuni da cewar, a bana, 8 ga watan Oktoba wannan shekerar da muke ciki itace ranar karshe ta biyan kudin kujeran aikin hajji kamar yadda hukumar kasar Saudi Arabia ta bayyana.

A sabili da haka nema Labbo yayi kira ga maniyyata aikin hajjin badi da su gaggauta biyan kudin ajiyar su na naira miliyan 8 da dubu dari 5 kamar yadda hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta bayyana.

Ahmed Labbo, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa kula da ayyukan hukumar a kowane lokaci.

NAHCON dai ta baiwa Jihar Jigawa kason kujeru fiye da 1,600 na maniyyatan aikin hajjin.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumomin Bada Agajin Gaggawa Sun Bada Horo Kan Aikin Ceto A Karamar Hukumar Auyo
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • An kama sojan bogi da ɓarayin mota 2 a Jigawa
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar