Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta ce, a ranar 19 ga wannan wata, ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya yi bayani game da yanayin tafiyar tattalin arzikin kasar Sin a watan Afrilu, inda kafofin watsa labaru na kasa da kasa suka yi amfani da kalmomi kamar “wuce zaton da aka yi” da kuma “ da karfi” wajen yabawa tattalin arzikin kasar Sin.

Mao Ning ta bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Laraba, inda ta ce, bisa yanayin tinkarar harajin kwastam mai yawa, kasar Sin ta tabbatar da bunkasar cinikayyar kasa da kasa.

A farkon watanni 4 na bana, yawan kudin kayayyakin shige da fice na kasar Sin ya karu da kashi 2.4 cikin dari, a cikinsu yawan kudin kayayyakin da aka fitar ya karu da kashi 7.5 cikin dari, lamarin da ya shaida cewa, Sin tana da karfin yin takara a duniya. Haka zalika, Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje, da sa kaimi ga kamfanonin kasashen waje da su kara samun ci gaba da wuce zaton da aka yi a kasar. Wadannan duka sun shaida cewa, Sin tana da karfi wajen tinkarar hadari da kalubale a fannoni daban daban. (Zainab Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan

Rasha ta zama ƙasa ta farko da a hukumance ta amince da gwamnatin ƙungiyar Taliban da ke mulkin ƙasar Afghanistan.

Wannan na zuwa ne bayan Rashar ta karɓi takardun shaidar kama aiki na sabon jakadan Afghanistan, wanda hakan ya sa ta zama ƙasa ta farko da ta amince da gwamnatin Taliban a ƙasar.

Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA Majalisar Mali ta ƙara wa Goita wa’adin mulkin shekara biyar

“Mun yi imani cewa wannan matakin na amincewa a hukumance da gwamnatin Daular Musulunci ta Afghanistan zai ba da damar haɓaka haɗin gwiwa mai amfani tsakanin ƙasashenmu a fannoni daban-daban,” in ji Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Afghanistan ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa jakadan Rasha Dmitry Zhirnov ya gana da Ministan Harkokin Wajen Taliban Amir Khan Muttaqi, inda ya isar da wannan matakin na gwamnatin Rasha da ke nuna “muhimmancin wannan mataki”.

Zhirnov ya bayyana wannan a matsayin “mataki mai tarihi wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Afghanistan ta ce: “Da wannan mataki, dangantakar ƙasashen biyu za ta ƙara faɗaɗa.”

Muttaqi ya nuna fatan cewa wannan zai haifar da ƙarin haɗin gwiwa da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin Afghanistan da Rasha.

Zhirnov ya shaida wa tashar talabijin ta gwamnati Rossiya-1 Shugaba Vladimir Putin ne ya ɗauki wannan matakin bisa shawarar Ministan Harkokin Wajen Rasha Sergey Lavrov. “Wannan yana nuna burin gaskiya na Rasha na kafa haɗin gwiwa mai ƙarfi da Afghanistan,” in ji shi.

Zuwa yanzu dai babu wata ƙasa mamba a Majalisar Ɗinkin Duniya da ta amince da gwamnatin riƙon ƙwarya ta Taliban tun dawowarta kan mulki a watan Agustan 2021.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
  • Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA