Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban
Published: 22nd, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta ce, a ranar 19 ga wannan wata, ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya yi bayani game da yanayin tafiyar tattalin arzikin kasar Sin a watan Afrilu, inda kafofin watsa labaru na kasa da kasa suka yi amfani da kalmomi kamar “wuce zaton da aka yi” da kuma “ da karfi” wajen yabawa tattalin arzikin kasar Sin.
Mao Ning ta bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Laraba, inda ta ce, bisa yanayin tinkarar harajin kwastam mai yawa, kasar Sin ta tabbatar da bunkasar cinikayyar kasa da kasa.
A farkon watanni 4 na bana, yawan kudin kayayyakin shige da fice na kasar Sin ya karu da kashi 2.4 cikin dari, a cikinsu yawan kudin kayayyakin da aka fitar ya karu da kashi 7.5 cikin dari, lamarin da ya shaida cewa, Sin tana da karfin yin takara a duniya. Haka zalika, Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje, da sa kaimi ga kamfanonin kasashen waje da su kara samun ci gaba da wuce zaton da aka yi a kasar. Wadannan duka sun shaida cewa, Sin tana da karfi wajen tinkarar hadari da kalubale a fannoni daban daban. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
EU ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria
Bayan sanarwar ba-zata da Amurka ta yi a makon da ya gabata, Tarayyar Turai ta ce za ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria.
Ministocin harkokin waje da ke taro a Brussels ne suka yanke shawarar dage dukkan takunkumin tattalin arzikin kan Siriya.
“Muna son taimakawa al’ummar Siriya wajen sake gina sabuwar Siriya,” in ji jami’ar kula da harkokin wajen Tarayyar Turai Kaja Kalas.
Tarayyar Turai ta kuma yi alkawarin bayar da Yuro biliyan biyu da rabi domin sake gina kasar.
Matakin dage wannan takunkumin da aka kakabawa gwamnatin Bashar al-Assad tun daga shekara ta 2011, zai bada damar sakin kadarorin kasar da har yanzu ke daskare, sannan kuma zai baiwa hukumomin kasar damar neman zuba jarin da suke bukata.