Fitattun dalibai akalla 12 ne  daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare  a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).

A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.

Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.

A cewarsa, an zabo daliban 12 ne  sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.

Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.

“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.

Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.

A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.

Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara ETF

এছাড়াও পড়ুন:

Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka bisa yawan bashin da Najeriya ke ciyowa da kuma yadda gwamnati ke facaka da kuɗaɗen.

Sarkin wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne, ya kuma bayyana cewa cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri, yana  mai cewa da Gwamnatin ba ta cire tallafin mai ba, da Najeriya ta daɗe da tsiyacewa.

“Adawata a ɓangaren shan man ne, saboda muna ba da aikin yi ga matatun mai a Turai. Muna ba da aikin ga masu tace ɗanyen man,” in ji Sarki Sanusi.

Da yake jawabi a Taron Adabi na Duniya na Kano (KAPFEST) da aka gudanar a Kano ranar Asabar, masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa ɗabi’ar yawan cin bashin Najeriya za ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasar na tsawon lokaci.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a Gombe

Masanin tattalin arzikin ya bayyana damuwa musamman kan yadda gwamnati ke kashe kuɗaɗen da ta ciyo bashin.

Zuwa ƙarshen watan Maris, yawan bashin da ake bin Najeriya ya haura Naira tiriliyan 150.

A yayin taron wanda cibiyar Poetic Wednesdays Initiative (PWI), ta shirya, Sarki Sanusi II ya ce, ya ce, “Ina muke kai wannan tulin bashin da muke ciyowa a ƙasar nan?

“Zan yi farin cikin ganin an yi amfani da kuɗaɗen a fannin ilmantar da matasanmu, saboda su ne za su biya. Amma bai kamata mu yi ciyo bashi muna lafta wa tattalin arzikin ƙasa ba tare da zuba jari a fannin ilmantar da waɗanda su ne za su biya bashin ba.

“Nan da shekara 20 za mu faɗa a matsala a dalikin cin bashi. Dole a zuba jari a fannin inganta rayuwarsu domin samar da abubuwa.”

Ya bayyana cewa Najeriya ba ta yi sa’ar shugabanni nagari ba a tsawon lokaci, yana mai cewa yawancin shugabannin ƙasar ragwage ne masu yawan kawo uzuri.

Sarki Sanusi II ya bayyana kyakkyawan shugabanci a matsayin muhimmin abin da zai ceto Najeriya daga halin da take ciki, wanda ya kira na rashin sa’a.

Da yake sukar yanayin koma-bayan Najeriya alhali wasu ƙasashe sun yi gaba ta fannin kimiyya da fasaha da ci-gaban zamani, Sarki Sanusi II ya buƙaci matsala da su tashi domin karɓar ragamar shugabancin ƙasar, yana mai jaddada cewa hakan abu mai yiwuwa ne idan matasan suka jajirce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya