Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar
Published: 18th, September 2025 GMT
Bayanai na cewa, wannan munduwa mai ɗimbin tarihi, mallakin Fir’auna Amenemope ne, yayin da ta yi ɓatan-dabo a gidan tarihin da ake adana da ita.
An rarraba hoton munduwar zinarin ga jami’an da ke aiki a kan iyakokin ƙasar daban-daban da suka haɗa da filayen jiragen sama da tashohin jiragen ruwa da zummar daƙile fasaƙaurinta zuwa ƙetare.
Munduwar mai ɗauke da ado na musamman, na da matuƙar daraja tun zamanin Fir’aunan, yayin da ake danganta ta da tsofaffin gumakan da aka yi bautar su a can baya, sannan an ce tana da ƙarfin warkarwa.
Munduwar na cikin jerin kayayyakin tarihin da ake shirin zuwa da su wani gagarumin taron baje-kolin kayayyakin tarihi a Italiya da za a fara gudanarwa a watan gobe.
Tuni aka kafa wani kwamiti domin gudanar da bincike kan sauran kayayyakin tarihin da ake da su a ƙasar domin tabbatar da cewa, suna nan daram.
Gidan tarihi na Masar shi ne mafi daɗewa a yanƙin Gabas ta Tsakiya, kuma yana ɗauke da kayayyaki daban-daban har guda dubu 170.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Masar
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.
Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA