Isra’ila na ci gaba da ragargaza Birnin Gaza ta sama da ƙasa
Published: 18th, September 2025 GMT
Dakarun sojan Isra’ila na ƙara nausawa cikin wani yanki mai cike da jama’a a birnin Gaza, yayin da suke ci gaba da kai farmaki ta ƙasa domin ƙwace iko da babban birnin mafi cunkoson jama’a.
Ana iya ganin yadda hayaƙi ya turnuke sararin samaniya yayin da sojojin ke harba makaman atilare da luguden bama-bamai.
Dubban mutane sun gudu, wasu kuma sun maƙale saboda haɗarin da ke tattare da guduwar. Sama da mutane sittin ne aka ce an kashe a jiya kadai.
Isra’ila ta ce tana gudanar da bincike kan rahotannin da ke cewa dakarunta sun kai hari kan asibitin yara na Gazan.
Ta ce tana son kubutar da mutanenta da Hamas ta rike da su, da kuma fatattakar mayaƙan Hamas 3,000 a wurin da ta bayyana a matsayin “tungar mayaƙan ta ƙarshe”.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Wannan mataki ne awanni kaɗan bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da Anyanwu da wasu mutane uku, lamarin da ya ƙara ta’azzaea rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar PDP.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA