Aminiya:
2025-09-19@12:14:19 GMT

Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda

Published: 19th, September 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta ce akalla mutane 1,666 mazauna jihar Legas sun rasa ransu ta hanyoyin da ba su dace ba, ciki har da kashe kansu, tsakanin farkon 2020 zuwa karshen 2024.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin likitan binciken gawarwaki na rundunar, ACP Samuel Keshinro, yayin gabatar da rahoton bincike kan kisan mata a wani taron da aka gudanar a jihar ranar Alhamis.

Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza

A cewar Keshinro, rahoton ya mayar da hankali ne kan abubuwan da suka shafi kisan kai, kashe kai, hatsarurruka da sauran hanyoyin mutuwa da ba su da alaka da cuta, domin wayar da kan jama’a da ƙarfafa fafutuka kan matsalar kisan mata.

Bayanan da aka raba a wajen taron sun nuna cewa daga cikin mutuwar 1,666, 350 mata ne, yayin da 1,306 kuma maza ne, sai mutum 10 da ba a iya tantance jinsinsu ba.

Keshinro ya ce an tattara bayanan ne domin samar da madogara mai ƙarfi wajen yanke shawara da kuma wayar da kan jama’a kan hatsarin kisan mata.

Ya ce bayanan sun nuna cewa mafi yawan kisan mata ana aikata su ne daga abokan rayuwarsu na kusa.

“Mun fito da abubuwan da muka gano ta amfani da bayanan da ke hannun ’yan sanda a ofishin CID na jihar. Mun gano cewa daga cikin mutuwar mata 350, kusan guda 70 kisan abokan zamansu ne.

“Wannan yana nuna irin raunin da mata ke ciki, musamman a inda ake tsammanin za su samu ƙauna da kariya. Kuma ya zo a daidai lokacin da Majalisar Dinkin Duniya ta ware ranar 25 ga watan Nuwamba a matsayin ranar yaki da cin zarafin mata.”

Ya kuma ba da shawarar a rungumi amfani da tsarin adana bayanai ta kwamfuta da kuma inganta hanyoyin tattara bayanai a binciken laifuka.

A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Legas, Olorundare Jimoh, ya bayyana cewa bisa ga bayanan da aka tattara cikin shekara guda, adadin kisan mata a jihar bai kai yadda ake tsammani ba idan aka kwatanta da yawan jama’ar jihar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi

Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mani Malam Mumini ya jajanta wa al’ummar karamar hukumar Gumi kan mumunan al’amuran da suka salwantar da rayukan mazauna kauyen Fas su 19 a makonnin da suka gabata.

 

Malam Mumini ya bayyana haka ne a lokacin da ya jagoranci wasu jami’an gwamnati da suka kai ziyarar jaje ga al’umma, inda ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da Majalisar Masarautar, da daukacin al’ummar Gumi.

 

Ya bayyana bala’in a matsayin mai raɗaɗi, yana mai jaddada cewa, gwamnatin jihar ta himmatu wajen magance matsalolin.

 

Mataimakin Gwamnan ya tuna cewa lamarin na farko ya faru ne a lokacin da mazauna kauyen cikin firgici kan harin da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai, suka shiga cikin wani jirgin ruwa wanda a karshe ya kife sakamakon kifewar da ya yi, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama.

 

Ya kuma bayyana cewa, a yayin da bala’i na biyu ya faru kwanaki bayan wata motar bus ta Homa dauke da ‘yan  daurin aure ta kutsa cikin kogin Gwalli a kan hanyar da ta wuce kan gada mai dauke da yashi, inda mutane 19 suka mutu.

 

Ya yi nuni da cewa, duk da cewa dan majalisar da ke wakiltar yankin ya gabatar da kudiri a kan munin yanayin gadar, amma har yanzu ana duba lamarin a lokacin da bala’in ya afku.

 

Mani Malam Mumini ya ce tuni gwamnatin jihar ta aike da tawagar injiniyoyi domin tantance gadar da kuma hanyoyin da suka hada da juna.

 

Wani shugaban al’umma a Gwalli ya yi kira da a kawo dauki cikin gaggawa tare da jaddada muhimman dabarun hana gadar ta ruguje nan gaba.

 

Shima da yake nasa jawabin mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara, Adamu Aliyu Gumi, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi ga al’umma, ya kuma yi kira da a gaggauta daukar mataki na gaggawa domin kaucewa afkuwar bala’o’i.

 

A yayin ziyarar, Mataimakin Gwamnan ya kuma kai gaisuwar ban girma ga Mai Martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan mai murabus, tare da jajanta masa bisa wannan al’amarin da aka samu.

 

A nasa jawabi, mai martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan ya bukaci gwamnatin jihar da ta hada kai da hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA domin samar wa majalisar jiragen ruwa na zamani domin rage yawaitar hadurran jiragen ruwa.

 

Mai shari’a Hassan ya koka da cewa, kwalekwalen katako na gargajiya da ake amfani da su a halin yanzu ba su da tsaro kuma suna tabarbarewa cikin sauri, suna jefa rayuka cikin hadari.

 

Sarkin ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa kudurin da ta dauka na magance matsalar rashin tsaro da kuma kalubalen da ke addabar jihar.

 

Tun da farko, shugaban karamar hukumar Gumi, Aminu Nuhu Falale, ya kuma bukaci a kara kaimi wajen samar da tsaro musamman a yankin Birnin Magaji, saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga.

 

Ya bayyana cewa, hatsarin kwale-kwale na karshe ya samo asali ne sakamakon firgici yayin da mutanen kauyen suka yi yunkurin tserewa daga hannun ‘yan bindiga, lamarin da ya kai ga kifewar kwale-kwalen.

 

COV/AMINU DALHATU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi
  • Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno