Aminiya:
2025-11-02@17:01:39 GMT

Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja

Published: 18th, September 2025 GMT

Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa lokacin da take kokarin tserewa daga harin ’yan bindiga a ƙauyen Allawa da ke ƙaramar hukumar Shiroro ta Jihar Neja.

Hakkin ya fito ne daga bakin Hakimin Bassa, Bagudu Amos, yayin wani taron tattaunawa da mata kan rikici da zaman lafiya mai taken: “Ƙarfafa Matakan Kare Fyade da Cin Zarafin Mata a Jihar Neja”.

Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya HOTUNA: Yadda dubban magoya baya suka yi dafifi don tarbar Fubara

Taron dai wata kungiya mai zaman kanta mai suna Tunani Initiative ce ta shira shi, tare da hadin gwiwar gidauniyar Dorothy Njemanze Foundation da kuma gidauniyar Foundation, domin ƙarfafa gwiwar mata wajen magance cin zarafin jinsi a jihar.

Hakimin ya ce mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa domin tserewa daga farmakin ’yan bindigar, ba tare da ta san cewa jaririn da ke bayanta ya riga ya mutu ba.

Ya ce lamarin da ya faru a shekarar 2023 na daga cikin abubuwan da ke ci wa mata ’yan gudun hijira tuwo a ƙwarya a kullum, inda ya ƙara da cewa yawancin matan ba su da gogewar ilimin da zai ba su damar tinkarar cin zarafin jinsi da ke tasowa sakamakon rashin tsaro.

Shugabar ƙungiyar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta ce ana buƙatar a ba mata dama wajen samar da zaman lafiya da warware rikice-rikice a Jihar Neja.

Ta yi kira ga mata da su haɗa kai don karya shingen da ke hana su yin tasiri a rayuwa.

Ta ce, “A Jihar Neja, kamar yadda ake fama da rashin tsaro a wasu wurare, mata su ne suka fi shan wahalar mafi yawan hare-hare da kashe-kashen da ake yi. Idan ’yan bindiga suka kai hari, yawanci maza ne ake kashewa, sai matan da aka bari su ɗauki nauyin sake gina iyali.

“Wadannan rawar da mata ke takawa ba a lura da ita yadda ya kamata. Saboda haka, wannan tattaunawa ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa rawar da mata ke takawa wajen samar da zaman lafiya da kuma magance cin zarafin jinsi a Jihar Neja,” in ji ta.

Daraktan Hukumar Kare Haƙƙin Dan Adam ta Jihar, Nuhu Muhammad, ya jaddada buƙatar ƙara yawan mata a majalisar dokoki ta jiha da ta ƙasa, domin samar da dokoki da manufofi da suka dace da bukatunsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jariri a Jihar Neja

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Labarai Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari