Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)
Published: 19th, September 2025 GMT
Sai yace “A’a ba haram ba ne, kawai dai mutanena ba su san shi ba ne.” Annabi (SAW) ya taɓa cewa kar a ci tafarnuwa a shigo masallaci, aka tambaye shi: “Ya Rasulallah haram ne?” Sai ya ce “A’a ba na haramta abin da Allah bai haramta ba, kawai dai ni ne ba na son shi”, ka ga bambancin ladabin malamai na wancan zamani da na yanzu, a yanzu duk abin da wani Malami ba ya so sai kawai ya haramta shi.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ma’aikin Allah ne, Annabin Allah ne, sannan kuma shugaban ƙasa ne a wancan lokacin, shi yake tsara dokokin ƙasa (constitution) na ƙasarsa (Sallallahu Alaihi Wasallam), don haka yana hana wasu abubuwan kuma ya halatta wasu abubuwan, kamar yanda aka taɓa tambayar Abdullahi ɗan Abbas, sai ya ce: “to wallahi ni ma doka kaza da kaza ban sani ba na wucingadi ne ko kuwa na dindindin ne”. Don haka, majalisar dokoki ba za ta ce “na haramta kaza” ba, sai dai ta ce “na hana kaza saboda dalili kaza”, to duk ranar da wannan dalilin ya ɗauke sai ka ji an janye wannan hanin kuma.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam shari’arsa ta zo a mai tafiya ce, shi cikamakon Ma’aika ne, cikamakon Annabawa ne, don haka komai nasa na har ƙarshen halitta ne, don haka ne ya zamo rahama ga halitta gaba ɗaya. Don haka babu wanda za ka je masa da faɗa ka tilasta masa ya karɓi ra’ayinka, Manzo ne, Ma’aiki ne ga duk duniya gaba ɗaya, ya zo ya daidaita addininsa a cikinmu, ya yaɗa zaman lafiya a cikinmu, ya yaɗa girmama ɗan Adam; dama abu biyu ne addini; Allah ya saka ma Shehu Ibrahim (RTA) da alheri, yana cewa: “abu biyu ne addini, Girmama Allah da tausayin ɗan Adam, wannan shine addini”, duk abin da za ka ga addini yana kira, za ka ga a kan waɗannan abubuwan biyun ne. Don haka suka ce: “duk addinin da ya kira ka zuwa cewa kar ka tausaya ma ɗan Adam to ba daga Allah yake ba”. Domin Allah shi ya halicci ɗan Adam ɗin nan, shi ya busa masa ransa, to kuwa Allah Tabaraka wa Ta’ala ba zai wulaƙanta ɗan Adam ɗin nan ba.
Mutum kansa idan ya ƙera tukwane, ba zai yadda haka kawai wani ya zo ya farfasa masa tukwanensa ba, haka idan ka sayi sabon abin hawa ba zaka yarda kawai wani ya zo ya farfasa maka shi ba, da yara sun zo suna wasan jifa a kusa da abin hawan ka zaka kore su ne, ba don kar su fasa maka kai ba ne, a’a, domin kar su fasa maka abin hawan nan naka, to ka ga ta yaya Allah shi kuwa zai bar halittarsa a zo ana aibata ta ana halaka ta? Wallahi mu ji tsoron Allah. Wannan ya jawo ake mayar da addininmu baya. Manzon Allah ya zo ya yaɗa zaman lafiya, ya yaɗa girmama ɗan Adam, ya yaɗa soyayya a tsakaninsu, ya yaɗa daidaito a tsakanin ƙabilu da jinsunan mu, ayar Alƙur’ani ta ce, “Ya ayyuhan nasu innaa khalaƙnakum min zakarin wa untha, wa ja’alnaakum shu’uban wa ƙaba’ila lita’arafu; inna akramakum indallahi atƙaakum”. Ma’anar wannan aya ta sama tana nufin ko da Bayahude ko Bamajuse ko kuma ɗan kowanne addini idan ya fi ka tsoron Allah, to fa ya fika a wajen Allah, domin Allah “ya ayyuhan nasu” ya ce ba “ya ayyuhal muslimuna” ba.
Akwai wani Bature, ya karanta littafan Annabawa da suka gabata da duk sauran littafan da ake cewa Allah ne ya saukar dasu, ya dudduba ya yi nazari, sai da Allah ya kawo shi Misra, ya haɗu da abokinsa sai ya sami ganin Kur’ani ta wajen abokin nan nasa kuma abokin ya tabbatar masa cewa shi ma wannan littafi daga Allah ne, sai ya ce to a ba shi ya duba (watau Alkur’ani mai fassara zuwa Ingilishi). Yana fara karantawa sai kuwa ya ce: “Haba! Yanzu na ji Allah ne yake magana! Amma duk waɗancan sauran littafan ina jin wani mutum ne abokina ko wani sarki mutum ne yake magana!”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kashe ’yan bindiga 19 yayin daƙile wani hari a Kano
Dakarun Rundunar Sojin Najeriya sun daƙile wani harin ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Shanono da ke Jihar Kano, inda suka yi nasarar hallaka 19 daga cikin ’yan ta’addan.
Bayanai sun ce sojojin ƙarƙashin rundunar haɗin gwiwa ta Operation MESA sun fafata da ‘yan bindigar ne da yammacin ranar Asabar bayan samun bayanan sirri kan motsinsu a yankunan Unguwar Tudu da Unguwar Tsamiya da Goron Dutse.
’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar NijeriyaA sanarwar da kakakin rundunar, Kyaftin Babatunde Zubairu, ya fitar, sojojin sun gaggauta kai samame yankin bayan samun rahoto, inda suka yi musayar wuta da ’yan bindigar.
“A yayin arangamar, an hallaka ’yan bindiga 19, kuma an ƙwato babura da dama da wayoyin salula guda biyu daga hannunsu,” in ji Kyaftin Zubairu.
Sai dai ya tabbatar da cewa sojoji biyu da ɗan sa-kai guda ɗaya sun rasu yayin fafatawar.
Kyaftin Zubairu ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da sintiri a yankin don kare al’ummomin da ke cikin haɗarin hare-haren masu satar shanu da sauran laifuka.
Rundunar ta kuma shawarci jama’a su kasance cikin shiri da lura, tare da kai rahoton duk wani motsi da ake zargin ba na halas ba ga jami’an tsaro mafi kusa.
A cewar kwamandan rundunar, Birgediya Janar Ahmed Tukur, Rundunar Sojin Najeriya na ƙoƙari wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Kano, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro.
An bayyana wannan aikin a matsayin wani ɓangare na ci gaba da kare yankunan karkara domin bai wa mazauna ƙwarin gwiwa a wuraren da ake fama da hare-haren ’yan bindiga.