Matatar Dangote ta sanar da dakatar da tsarin ɗaukar mai kai tsaye daga matatar, inda ya ce wannan mataki zai fara aiki daga ranar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025. Sanarwar ta bayyana cewa matakin zai hana masu siye marasa rajista shiga wajen saye kai tsaye tare da ƙarfafa amfani da tsarin kai wa kyau bayan saye (Free Delivery Scheme).

A cewar kamfanin, wannan sauyin wani gyaran aiki ne don inganta tsari, tare da tabbatar da cewa manyan cibiyoyin lafiya da muhimman wurare suna ci gaba da samun isasshen mai. Matatar Dangote ta kuma umarci a dakatar da dukkan biyan kuɗi da ya shafi ɗaukar mai kai tsaye, inda ta ce duk wani kuɗi da aka biya bayan wannan rana ba za a karɓa ba.

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Sai dai matakin ya zo ne a daidai lokacin da ake samun saɓani tsakanin matatar, da NUPENG da DAPPMAN. Yayin da NUPENG ke zargin kamfanin da ƙin yarda da ƙungiyantar da direbobinta, DAPPMAN na ganin tsarin kai wa kyauta zai tilasta ‘yan kasuwa su dogara da motocin Dangote a farashi mai tsada.

Amma a cewar kamfanin, tsarin ya ƙunshi dabarar kare rabon man fetur daga karkatarwa da kuma tabbatar da wadatar mai a kasuwa. Masana sun yi gargaɗin cewa dakatarwar za ta fi shafar ‘yan kasuwa masu zaman kansu da gidajen mai da ba su shiga tsarin kai wa kyauta ba, waɗanda suka dogara da ɗaukar mai kai tsaye daga matatar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike

Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

Sauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.

An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.

Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.

Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.

Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike